Home General Majilisar Jihar Niger ta karyata Sojojin Nijeriya

Majilisar Jihar Niger ta karyata Sojojin Nijeriya

‘Yan bindiga dake jihar Niger a tsakiyar Nijeriya sun yi awon gaba da mutane a 20 a cikin motoci 5 da suka tare a hanyar Mariga-Kontagora.

kakakin majalisar jihar Niger, dan majalisa mai wakiltar mazabar mariga Barister Abdulmalik Sarkin-Daji ne ya tabbatar da hakan yayin da yake ganawa da manema labarai.

yace labarin ya faru ne a ranar alhamis yayin da ‘yan bindigar suka tare hanyar Mariga-kontagora tsakanin Babban-Lamba da Beri.

wannan dai jawabi na kakakin majalisar na matsayin martani ga rundunar sojojin Nijeriya, wadda ta musanta cewa ‘yan ta’addan basu mamaye wajen horar da dakarunta dake karamar hukumar Kontagora ba wanda yanzu haka sun fafadada zuwa karamar hukumar Mariga.

sarkin daji yace iyalen wadanda aka yi garkuwa da su, sun sha kai kudin fansa ga ‘yan ta’addan, wanda kuma wajen horar da dakarun sojojin Najeriya ne wajen da ake kai kudin fansar.

yace wadanda aka sako din sun bayyanawa iyalen su cewa, an ajje su ne a dajin da babub nesa da barikin sojoji ta Kontagora.

haka kuma ya kara da cewa Fasinjojin da ‘yan ta’addan suka kama ranar alhamis sun kai su ne zuwa wannan daji, in da ya bukaci dakarun sojojin sun sami bayani na gaskiya domin su fitar da ‘yan bindigar daga cikin daji.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp