Home General Majilisar Jihar Niger ta karyata Sojojin Nijeriya

Majilisar Jihar Niger ta karyata Sojojin Nijeriya

‘Yan bindiga dake jihar Niger a tsakiyar Nijeriya sun yi awon gaba da mutane a 20 a cikin motoci 5 da suka tare a hanyar Mariga-Kontagora.

kakakin majalisar jihar Niger, dan majalisa mai wakiltar mazabar mariga Barister Abdulmalik Sarkin-Daji ne ya tabbatar da hakan yayin da yake ganawa da manema labarai.

yace labarin ya faru ne a ranar alhamis yayin da ‘yan bindigar suka tare hanyar Mariga-kontagora tsakanin Babban-Lamba da Beri.

wannan dai jawabi na kakakin majalisar na matsayin martani ga rundunar sojojin Nijeriya, wadda ta musanta cewa ‘yan ta’addan basu mamaye wajen horar da dakarunta dake karamar hukumar Kontagora ba wanda yanzu haka sun fafadada zuwa karamar hukumar Mariga.

sarkin daji yace iyalen wadanda aka yi garkuwa da su, sun sha kai kudin fansa ga ‘yan ta’addan, wanda kuma wajen horar da dakarun sojojin Najeriya ne wajen da ake kai kudin fansar.

yace wadanda aka sako din sun bayyanawa iyalen su cewa, an ajje su ne a dajin da babub nesa da barikin sojoji ta Kontagora.

haka kuma ya kara da cewa Fasinjojin da ‘yan ta’addan suka kama ranar alhamis sun kai su ne zuwa wannan daji, in da ya bukaci dakarun sojojin sun sami bayani na gaskiya domin su fitar da ‘yan bindigar daga cikin daji.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp