Home General Majilisar Jihar Niger ta karyata Sojojin Nijeriya

Majilisar Jihar Niger ta karyata Sojojin Nijeriya

‘Yan bindiga dake jihar Niger a tsakiyar Nijeriya sun yi awon gaba da mutane a 20 a cikin motoci 5 da suka tare a hanyar Mariga-Kontagora.

kakakin majalisar jihar Niger, dan majalisa mai wakiltar mazabar mariga Barister Abdulmalik Sarkin-Daji ne ya tabbatar da hakan yayin da yake ganawa da manema labarai.

yace labarin ya faru ne a ranar alhamis yayin da ‘yan bindigar suka tare hanyar Mariga-kontagora tsakanin Babban-Lamba da Beri.

wannan dai jawabi na kakakin majalisar na matsayin martani ga rundunar sojojin Nijeriya, wadda ta musanta cewa ‘yan ta’addan basu mamaye wajen horar da dakarunta dake karamar hukumar Kontagora ba wanda yanzu haka sun fafadada zuwa karamar hukumar Mariga.

sarkin daji yace iyalen wadanda aka yi garkuwa da su, sun sha kai kudin fansa ga ‘yan ta’addan, wanda kuma wajen horar da dakarun sojojin Najeriya ne wajen da ake kai kudin fansar.

yace wadanda aka sako din sun bayyanawa iyalen su cewa, an ajje su ne a dajin da babub nesa da barikin sojoji ta Kontagora.

haka kuma ya kara da cewa Fasinjojin da ‘yan ta’addan suka kama ranar alhamis sun kai su ne zuwa wannan daji, in da ya bukaci dakarun sojojin sun sami bayani na gaskiya domin su fitar da ‘yan bindigar daga cikin daji.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp