Home General Gwamnan Kano ya haramta kalmar “Abba Tsaya Da Kafarka”

Gwamnan Kano ya haramta kalmar “Abba Tsaya Da Kafarka”

Gwamnan Jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ce cin fuska ne fada masa kalmar “Abba Tsaya Da Kafarka” kamar yanda wasu suke Faɗa.

Ya bayyana hakan ne a yayin da yake ganawa da manema labarai a daren Laraba a fadar Gwamnatin Jihar Kano.

Abba ya ce shekaru 40 na kwashe tare da Sanata Rabiu Musa Kwankwaso Kuma Muna Tare Dashi har yanzu.

“Ina mamakin yadda wasu suke cewa na Tsaya da Kafata Kuma wanna Cin Fuska ne gare ni, domin kuwa Kwankwaso Mai gidana ne Muna zaune Lafiya dashi Dan Haka Babu Wata Baraka a tsakanin mu”

“Daga Yau Laraba 6-11-2024 Duk Wani jami’in Gwamnati ko abokan Arziki ko masoya na haramta  masa Kara Cewa na Tsaya da Kafata.

” Kwankwaso shine Jagoran mu Kuma shine Shugaban mu, Amma Saboda son zuciyar Wasu Suke Kokarin Kawo Mana rikici a Jam’iyyar NNPP.”

“Dan Haka nake Muku rantsuwa da Cewa wallahi bani da masaniya akan abinda Wasu Ke Cewa wai Akwai rigima tsakanina da Kwankwaso.”

Abba ya ce yayi niyyar maka jaridar da ta wallafa cewa yaki daukar kiran Kwankwaso a kotu amma wasu dalilai ne suka hana.

“Nayi niyyar zuwa Kotu akan Cewa wai Kwankwaso ya kirani sau 33 ban dauka ba, to amma na hakura Saboda Yadda nake girmama Yan Jarida”

PRNigeria hausa
 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp