Home General Gwamnan Kano ya haramta kalmar “Abba Tsaya Da Kafarka”

Gwamnan Kano ya haramta kalmar “Abba Tsaya Da Kafarka”

Gwamnan Jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ce cin fuska ne fada masa kalmar “Abba Tsaya Da Kafarka” kamar yanda wasu suke Faɗa.

Ya bayyana hakan ne a yayin da yake ganawa da manema labarai a daren Laraba a fadar Gwamnatin Jihar Kano.

Abba ya ce shekaru 40 na kwashe tare da Sanata Rabiu Musa Kwankwaso Kuma Muna Tare Dashi har yanzu.

“Ina mamakin yadda wasu suke cewa na Tsaya da Kafata Kuma wanna Cin Fuska ne gare ni, domin kuwa Kwankwaso Mai gidana ne Muna zaune Lafiya dashi Dan Haka Babu Wata Baraka a tsakanin mu”

“Daga Yau Laraba 6-11-2024 Duk Wani jami’in Gwamnati ko abokan Arziki ko masoya na haramta  masa Kara Cewa na Tsaya da Kafata.

” Kwankwaso shine Jagoran mu Kuma shine Shugaban mu, Amma Saboda son zuciyar Wasu Suke Kokarin Kawo Mana rikici a Jam’iyyar NNPP.”

“Dan Haka nake Muku rantsuwa da Cewa wallahi bani da masaniya akan abinda Wasu Ke Cewa wai Akwai rigima tsakanina da Kwankwaso.”

Abba ya ce yayi niyyar maka jaridar da ta wallafa cewa yaki daukar kiran Kwankwaso a kotu amma wasu dalilai ne suka hana.

“Nayi niyyar zuwa Kotu akan Cewa wai Kwankwaso ya kirani sau 33 ban dauka ba, to amma na hakura Saboda Yadda nake girmama Yan Jarida”

PRNigeria hausa
 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Rahoton ‘Yan Sanda ya Danganta Kashi 70% na Laifuka a Kano da Shaye-Shayen Miyagun Ƙwayoyi, Ya Gano Mutane 513 da ake Zargin Masu Safara NePantami Ya Samu Karfin Gwiwa Yayin Da Jama'a Ke Taya Shi Murna a Lokacin Ziyarar Ayyuka a GombeMa’aikatar Tsaro ta yi Karin Bayani Kan Yarjejeniyar Yaki da Ta’addanci da Turkiyya, ta Karyata Zargin ‘Jihadi’Tinubu na Neman Amincewar Majalisar Dattawa kan Sabon Rancen $516.3mGadon Mulkin Gombe: Wa Ke Jin Tsoron Tasirin Pantami Daga Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Masu Kera Makamai ba Bisa Ka'ida ba a Filato, Sun Kama Wadanda ake Zargi da Ta'addanci a NijarShin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa Malami
X whatsapp