Home General Gwamnan Kano ya haramta kalmar “Abba Tsaya Da Kafarka”

Gwamnan Kano ya haramta kalmar “Abba Tsaya Da Kafarka”

Gwamnan Jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ce cin fuska ne fada masa kalmar “Abba Tsaya Da Kafarka” kamar yanda wasu suke Faɗa.

Ya bayyana hakan ne a yayin da yake ganawa da manema labarai a daren Laraba a fadar Gwamnatin Jihar Kano.

Abba ya ce shekaru 40 na kwashe tare da Sanata Rabiu Musa Kwankwaso Kuma Muna Tare Dashi har yanzu.

“Ina mamakin yadda wasu suke cewa na Tsaya da Kafata Kuma wanna Cin Fuska ne gare ni, domin kuwa Kwankwaso Mai gidana ne Muna zaune Lafiya dashi Dan Haka Babu Wata Baraka a tsakanin mu”

“Daga Yau Laraba 6-11-2024 Duk Wani jami’in Gwamnati ko abokan Arziki ko masoya na haramta  masa Kara Cewa na Tsaya da Kafata.

” Kwankwaso shine Jagoran mu Kuma shine Shugaban mu, Amma Saboda son zuciyar Wasu Suke Kokarin Kawo Mana rikici a Jam’iyyar NNPP.”

“Dan Haka nake Muku rantsuwa da Cewa wallahi bani da masaniya akan abinda Wasu Ke Cewa wai Akwai rigima tsakanina da Kwankwaso.”

Abba ya ce yayi niyyar maka jaridar da ta wallafa cewa yaki daukar kiran Kwankwaso a kotu amma wasu dalilai ne suka hana.

“Nayi niyyar zuwa Kotu akan Cewa wai Kwankwaso ya kirani sau 33 ban dauka ba, to amma na hakura Saboda Yadda nake girmama Yan Jarida”

PRNigeria hausa
 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp