Home General CBN ya ci tarar bankuna saboda rashin saka kuɗi a ATM

CBN ya ci tarar bankuna saboda rashin saka kuɗi a ATM

Babban bankin Najeriya CB ya ci tarar wasu bankunan kasuwanci na Najeriya saboda samun kuɗi a na’urorin cire kuɗi na ATM ɗinsu a lokacin bukuwan ƙarshen shekara.

Babban bankin ya tarar naira miliyan 150 ne kan kowane banki da ya samu da laifin, kuma bankunan sun haɗa da Fidelity da First Bank Plc da Keystone da Union da Globus da Providus da Zenith Bank da UBA da Sterling tarar naira miliyan 150.

A wata sanarwa da aka miƙa wa bankunan, an ce za a zare kuɗaɗen ne kai tsare daga asusun ajiyan bankunan da ke babban bankin,” kamar yadda tashar Channels ta ruwaito.

“CBN ba za ta yi ƙasa a gwiwa ba wajen cin tarar duk wani bankin da ya karya dokar tabbatar da yalwatar kuɗaɗe,” kamar yadda mataimakin daraktan hulɗa da jama’a na bankin, Hakama Sidi Ali ya tabbatar.

Ya kuma ƙara da cewa za su cigaba da bibiyar masu ɓoye tsabar kuɗaɗe a bankuna da masu POS.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp