Home General Mun samar wa gwamnatin tarayya naira tiriliyan 10 a 2024 – NNPCL

Mun samar wa gwamnatin tarayya naira tiriliyan 10 a 2024 – NNPCL

Kamfanin man fetur na Najeriya NNPCL ya ce ya zuwa watan Satumban shekarar 2024, kuɗin da ya samar wa gwamnatin tarayya ya kai naira tiriliyan 100.

Shugaban kamfanin, Mele Kyari ne ya sanar da hakan a lokacin da ya bayyana a gaban kwamitin kuɗi na majalisar dattawa, inda yake kare kasafin kuɗin kamfanin na bana.

Ya ce NNPCL na fitar da bayanan asusunsa na shekara-shekara, “Hada-hadarmu a fili suke, kuma muna bayyana duk harkokin kuɗin da muka yi a fili ba tare da nuƙu-nuƙu ba,” in ji shi kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito.

Kyari ya ce kamfanin na NNPCL ne kamfanin da ya fi biyan haraji, kuma wanda ya fi samar da riba ga masu zuba jari.

Sai dai ya ce sai sun zauna tare da daraktocin kamfanin ne za su iya fitar da hasashen kuɗin da za su samar a bana.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp