Home General Ana fargabar mutuwar tarin Sojin Najeriya a wani sabon harin ISWAP

Ana fargabar mutuwar tarin Sojin Najeriya a wani sabon harin ISWAP

Wasu rahotanni daga jihar Borno da ke arewa maso gabashin Najeriya sun ce ƴan ta’adda sun sake farmakar ayarin Sojin ƙasar da ke kan hanyarsu ta laluben gawarwakin manoma 40 da ISWAP ta hallaka a garin Dumba na yankin Baga da ke ƙaramar hukumar Kukawa a jihar.

Wasu majiyoyi daga yankin sun tabbatar da cewa mayaƙan ISWAP ne suka ƙaddamar da harin kuma har kawo yanzu babu cikakkun alƙaluman sojojin da aka rasa a wannan farmaki.

Wata majiya daga ɓangaren ƴan sa kan ta bayyana cewa tun da farko adadi mai yawa na Sojin Najeriya tare da ƴan sakai 54 ciki har da mafarauta ne suka shiga dajin don laluben gawarwakin sai dai har zuwa yanzu ɗan sa kai 1 ne tal ya dawo cikin Baga a galabaice.

A cewar bayanai sun ce da farko sojojin sun so daƙile harin ƴan ta’addan amma kuma yawan makaman da mayaƙan ke ɗauke da shi ya tilasta musu ja da baya.

Rahotanni sun ce babu tabbacin Soji nawa suka mutu ko kuma nawa suka jikkata haka zalika a ɓangaren mayaƙan na sa kai lura da cewa hatta mutum guda da ya dawo cikin gari baya cikin hayyacinsa da zai iya bayar da labarin abin da ya faru.

Sai dai wata majiya daga ɓangaren Sojin Najeriya ta ce tuni wasu daga cikin dakarun na ta suka dawo sansaninsu da ke Baga.

A cewar majiyoyin Sojin sun birne 15 daga cikin manoman da ƴan ta’addam suka kashe sai sun haɗu da farmaki a lokacin da suka kai tsakiyar hanya a ƙoƙarinsu na isa Dumba, amma sun ci gaba da tafiya bana kawar da barazanar ƴan ta’addan.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp