Home General Gwamnatin Kano na shirin kafa kwamitin bincike kan kungiyoyin masu zaman kansu...

Gwamnatin Kano na shirin kafa kwamitin bincike kan kungiyoyin masu zaman kansu NGOs

Gwamnatin Jihar Kano ta sanar da shirin gudanar da bincike mai zurfi kan ayyukan ƙungiyoyi masu zaman kansu (NGOs) a jihar, domin tabbatar da cewa sun yi daidai da al’adun Musulunci da kuma ka’idojin zamantakewar al’umma.

Matakin ya zo ne bayan bayyanar wata ƙungiya da ake zargi da yada ra’ayin auren jinsi, abin da ya haifar da cece-kuce a cikin jihar.

Gwamnatin ta ce za a tantance ayyukan waɗannan ƙungiyoyi, musamman ta hanyar duba tushen samun kuɗinsu, da shugabanninsu, da kuma bin dokokin ƙasa.

A cikin wannan tsari, za a yi amfani da ka’idojin ƙasa da na duniya kamar dokokin FATF (wanda ke yaƙi da satar kuɗi), da dokokin Kwamitin Tsaro na Majalisar Ɗinkin Duniya, da kuma Dokar Kamfanoni ta Najeriya (CAMA 2020) don tabbatar da gaskiyar ayyukan ƙungiyoyin.

Gwamnati ta bayyana cewa manufar ita ce kare al’adun gargajiya na al’umma, da ƙarfafa gaskiya, da kuma hana amfani da kuɗin kasashen waje don ayyukan da suka shafi tsaro.

Matakin ya zo ne tare da naɗin kwamishinan ma’aikatar yaɗa labarai ta jihar Kano Comrade Ibrahim Abdullahi Waiya, wanda Gwamna Abba Kabir Yusuf ya zaba a matsayin wanda zai jagoranci aiwatar da wannan binciken.

Sai dai wasu ƙungiyoyi masu zaman kansu sun nuna adawa da wannan yunkuri, inda gwamnati ta yi zargin cewa masu adawar na tsoron bayyana “manufofinsu na ɓoye” da suka saba wa al’adun jihar Kano.

Gwamnati ta ce ƙungiyoyin da ke aiki bisa doka ba za su ji tsoron wannan bincike ba, yayin da binciken zai ƙara ƙarfafa amincewar jama’a da su.

Gwamnatin ta bayyana cewa ƙin yarda da wannan tsari na iya nuna wata manufa ta ɓatanci da rashin gaskiya, kamar satar kuɗi ko karya ka’idoji.

Dr. Abraman Sunday, shine shugaban ƙungiyar fararen hula ta Integrity Group, ya yaba wa matakin, yana mai cewa zai inganta aikin ƙungiyoyi masu zaman kansu.

Ana sa ran za a fara aiwatar da wannan tsari cikin ‘yan makonnin nan.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp