Home General Dakarun Najeriya sun kashe ‘yan ta’adda 82 tare da kama 198 a...

Dakarun Najeriya sun kashe ‘yan ta’adda 82 tare da kama 198 a mako guda

Shelkwatar tsaron Najeriya ta ce dakarunta sun kashe ƴan ta’adda 82  tare da kama guda 198, suka kuma ceto mutane 93 da aka yi garkuwa da su a cikin mako guda da ya wuce a sassan ƙasar.

Daraktan yaɗa labarai na ma’aikatar, Manjo Janar Markus Kangye,  ne ya bayyana haka a Abuja,  a yayin da ya ke yi wa manema labarai bitar nasarorin  da dakarun ƙasar suka samu.

Kangye  yace dakarun sun kuma ƙwace ɗimbim makamai da ababen hawa a daga ƴan ta’addan a samamen da suka yi daga ranar 14 zuwa 21 ga watan Fabrairu.

Ya ce dakarun sun ƙwace bindigogi da suka haɗa da AK47 guda 46, bindigogin da aka ƙera a gida guda 18, sai bindigogin zari-ruga guda 19 da harshasai sama 1,200.

Kakakin ma’aikatar tsaron ya ƙara da cewa ƴan ta’addda 41 sun miƙa wuya ga dakarun rundunar Operation HADIN KAI a yankin arewa maso gabashin ƙasar, kuma daga cikin su akwai manya baligai 41, sai yara 19.

Janar Kangye ya ƙara da cewa dakarun na Najeriya sun kama masu satar mai a yankin Kudu maso Kudancin ƙasar, sun kuma daƙile satar da kiyasta darajarta ta kai naira 587.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp