Home General Tinubu ya nada sabon Akanta Janar a Nijeriya

Tinubu ya nada sabon Akanta Janar a Nijeriya

Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya naɗa Shamsedeen Babatunde Ogunjimi, a matsayin sabon Akanta Janar na ƙasar.

Mashawarcin shugaban ƙasar kan yaɗa labarai da tsare-tsare, Boyo Onanuga ne ya sanar da hakan ta cikin wata sanarwa da ya sanyawa hannu, inda ya ce shugaban ya naɗa shi ne bayan an tantance shi.

Nadin nasa, wanda aka amince da shi a yau, zai fara aiki ne daga ranar 7 ga Maris 2025, ranar da wanda yake kan mukamin Oluwatoyin Madehin zai yi ritaya.

Sanarwar ta ce sai da shugaba Tinubu ya sa aka bi matakai daban-daban, wajen tantance Ogunjimi mai shekaru 57 domin tabbatar da ƙwarewarsa.

Ogunjimi ya kammala karatunsa na digirin farko a Jami’ar Nsukka, a shekarar 1990, inda ya karanci harkar akanta, sannan kuma ya sami digiri na biyu a fannin tsumi (Accounting) a Jami’ar Legas, a inda yanzu haka Mamba ne a Cibiyar Akantoci ta Najeriya.

A ƙarshe Tinubu ya buƙace shi da ya dage wajen sauke nauyin da ya rataya a wuyansa na yi wa Najeriya hidima cikin gaskiya, ƙwarewa, da sadaukarwa ga hidimar ƙasar.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp