Home General Matatar Ɗangote za ta maida wa kwastomominta naira 65 kan kowace lita...

Matatar Ɗangote za ta maida wa kwastomominta naira 65 kan kowace lita man fetir

Matatar Dangote

Wanan mataki dai ya biyo bayan sanarwar da kamfanin ya yi na rage farashin litar man fetur, inda ya ce za a rinƙa siyar da ita kan naira 825 saɓanin naira 890.

A cikin wata sanarwa da matatar ta fitar a ƙarshen mako, ta tabbatar da cewar za ta maida wa duk wani ɗan kasuwar naira 65 kan kowa ce lita da ya siya, a cikin sama da tan dubu ɗari 2 da aka saida wa ƴan kasuwa, kan Naira 890 bayan sanar da sabon farashin na Naira 825.

Matatar ta Ɗangote ta buƙaci waɗanda suka siya litar man fetur sama da naira 825 bayan sanarwar rage farashin, a hannun abokan hulɗarta AP da Heyden da kuma MRS a duk faɗin Najeriya, su kai wa kamfanin risitinsu don maida musu da kuɗin da aka ƙara musu, wanda hakan ya sa matatar ta Ɗangote, za ta yi asarar Naira biliyan 16, a ƙoƙarinta na sauƙaƙa wa ƴan Najeriya.

Wannan matakin, da ya fara aiki a ranar 27 ga Fabrairu 2025, ya tabbatar da cewa babu wani abokin kasuwancinmu da zai yi asara saboda rage farashin da muka yi. Abu mai mahimmanci kuma shi ne, ragin farashin man fetur ɗin ya fara aiki nan take, don amfanin al’ummar Najeriya.

Matatar ta Dangote ta kuma yi ala wadai da duk wani mataki da wani zai ɗauka don daƙile walwalar ƴan Najeriya, ta hanyar sai da makamashin sama da naira 825 kan kowa ce lita.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp