Wanan mataki dai ya biyo bayan sanarwar da kamfanin ya yi na rage farashin litar man fetur, inda ya ce za a rinƙa siyar da ita kan naira 825 saɓanin naira 890.
A cikin wata sanarwa da matatar ta fitar a ƙarshen mako, ta tabbatar da cewar za ta maida wa duk wani ɗan kasuwar naira 65 kan kowa ce lita da ya siya, a cikin sama da tan dubu ɗari 2 da aka saida wa ƴan kasuwa, kan Naira 890 bayan sanar da sabon farashin na Naira 825.
Read Also:
Matatar ta Ɗangote ta buƙaci waɗanda suka siya litar man fetur sama da naira 825 bayan sanarwar rage farashin, a hannun abokan hulɗarta AP da Heyden da kuma MRS a duk faɗin Najeriya, su kai wa kamfanin risitinsu don maida musu da kuɗin da aka ƙara musu, wanda hakan ya sa matatar ta Ɗangote, za ta yi asarar Naira biliyan 16, a ƙoƙarinta na sauƙaƙa wa ƴan Najeriya.
Wannan matakin, da ya fara aiki a ranar 27 ga Fabrairu 2025, ya tabbatar da cewa babu wani abokin kasuwancinmu da zai yi asara saboda rage farashin da muka yi. Abu mai mahimmanci kuma shi ne, ragin farashin man fetur ɗin ya fara aiki nan take, don amfanin al’ummar Najeriya.
Matatar ta Dangote ta kuma yi ala wadai da duk wani mataki da wani zai ɗauka don daƙile walwalar ƴan Najeriya, ta hanyar sai da makamashin sama da naira 825 kan kowa ce lita.










