Home General Matatar Ɗangote za ta maida wa kwastomominta naira 65 kan kowace lita...

Matatar Ɗangote za ta maida wa kwastomominta naira 65 kan kowace lita man fetir

Matatar Dangote

Wanan mataki dai ya biyo bayan sanarwar da kamfanin ya yi na rage farashin litar man fetur, inda ya ce za a rinƙa siyar da ita kan naira 825 saɓanin naira 890.

A cikin wata sanarwa da matatar ta fitar a ƙarshen mako, ta tabbatar da cewar za ta maida wa duk wani ɗan kasuwar naira 65 kan kowa ce lita da ya siya, a cikin sama da tan dubu ɗari 2 da aka saida wa ƴan kasuwa, kan Naira 890 bayan sanar da sabon farashin na Naira 825.

Matatar ta Ɗangote ta buƙaci waɗanda suka siya litar man fetur sama da naira 825 bayan sanarwar rage farashin, a hannun abokan hulɗarta AP da Heyden da kuma MRS a duk faɗin Najeriya, su kai wa kamfanin risitinsu don maida musu da kuɗin da aka ƙara musu, wanda hakan ya sa matatar ta Ɗangote, za ta yi asarar Naira biliyan 16, a ƙoƙarinta na sauƙaƙa wa ƴan Najeriya.

Wannan matakin, da ya fara aiki a ranar 27 ga Fabrairu 2025, ya tabbatar da cewa babu wani abokin kasuwancinmu da zai yi asara saboda rage farashin da muka yi. Abu mai mahimmanci kuma shi ne, ragin farashin man fetur ɗin ya fara aiki nan take, don amfanin al’ummar Najeriya.

Matatar ta Dangote ta kuma yi ala wadai da duk wani mataki da wani zai ɗauka don daƙile walwalar ƴan Najeriya, ta hanyar sai da makamashin sama da naira 825 kan kowa ce lita.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp