Home General Matatar Ɗangote za ta maida wa kwastomominta naira 65 kan kowace lita...

Matatar Ɗangote za ta maida wa kwastomominta naira 65 kan kowace lita man fetir

Matatar Dangote

Wanan mataki dai ya biyo bayan sanarwar da kamfanin ya yi na rage farashin litar man fetur, inda ya ce za a rinƙa siyar da ita kan naira 825 saɓanin naira 890.

A cikin wata sanarwa da matatar ta fitar a ƙarshen mako, ta tabbatar da cewar za ta maida wa duk wani ɗan kasuwar naira 65 kan kowa ce lita da ya siya, a cikin sama da tan dubu ɗari 2 da aka saida wa ƴan kasuwa, kan Naira 890 bayan sanar da sabon farashin na Naira 825.

Matatar ta Ɗangote ta buƙaci waɗanda suka siya litar man fetur sama da naira 825 bayan sanarwar rage farashin, a hannun abokan hulɗarta AP da Heyden da kuma MRS a duk faɗin Najeriya, su kai wa kamfanin risitinsu don maida musu da kuɗin da aka ƙara musu, wanda hakan ya sa matatar ta Ɗangote, za ta yi asarar Naira biliyan 16, a ƙoƙarinta na sauƙaƙa wa ƴan Najeriya.

Wannan matakin, da ya fara aiki a ranar 27 ga Fabrairu 2025, ya tabbatar da cewa babu wani abokin kasuwancinmu da zai yi asara saboda rage farashin da muka yi. Abu mai mahimmanci kuma shi ne, ragin farashin man fetur ɗin ya fara aiki nan take, don amfanin al’ummar Najeriya.

Matatar ta Dangote ta kuma yi ala wadai da duk wani mataki da wani zai ɗauka don daƙile walwalar ƴan Najeriya, ta hanyar sai da makamashin sama da naira 825 kan kowa ce lita.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp