Home General Hare-haren Sojin Somalia sun hallaka mayaƙan al Shabaab fiye da 40

Hare-haren Sojin Somalia sun hallaka mayaƙan al Shabaab fiye da 40

Wasu bayana na bayyana cewa a kalla Mayaƙan al Shabab fiye da 40 ne suka mutu a wani gumurzu tsakaninsu da dakarun Sojin Somalia a ƙarshen mako, dakarun gwamnatin dai na ci gaba da samun galabar mafi girma a baya-bayan nan.

Sanarwar da rundunar Sojin Somalia ta wallafa a shafinta na X aka kuma sanar a gidan talabijin mallakin gwamnati a daren Lahadi, ta ce dakarunta sun hallaka mayaƙan fiye da 40 a yankin Hirshabelle.

Sanarwar ta ci gaba da cewa, dakarun Sojin sun ƙaddamar da hare-haren da taimakon dakarun ƙasashe da ke taimaka musu a yaƙi da al Shabaab ta yadda suka yi musu ƙawanya a maɓoyarsu da ke Biya Cadde a yankin na Hirshabelle.

Rundunar Sojin ta Somalia ta ce har zuwa yanzu dakarun na ci gaba da luguden wuta a maɓoyar mayaƙan na al Shabaab.

A baya-bayan nan Sojojin Somalia na samun nasara kan mayaƙan al Shabaab inda ko a watan jiya ta hallaka da dama daga cikinsu kwanaki bayan Amurka ta musu luguden wuta da jiragen yaƙi.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp