Home General Hare-haren Sojin Somalia sun hallaka mayaƙan al Shabaab fiye da 40

Hare-haren Sojin Somalia sun hallaka mayaƙan al Shabaab fiye da 40

Wasu bayana na bayyana cewa a kalla Mayaƙan al Shabab fiye da 40 ne suka mutu a wani gumurzu tsakaninsu da dakarun Sojin Somalia a ƙarshen mako, dakarun gwamnatin dai na ci gaba da samun galabar mafi girma a baya-bayan nan.

Sanarwar da rundunar Sojin Somalia ta wallafa a shafinta na X aka kuma sanar a gidan talabijin mallakin gwamnati a daren Lahadi, ta ce dakarunta sun hallaka mayaƙan fiye da 40 a yankin Hirshabelle.

Sanarwar ta ci gaba da cewa, dakarun Sojin sun ƙaddamar da hare-haren da taimakon dakarun ƙasashe da ke taimaka musu a yaƙi da al Shabaab ta yadda suka yi musu ƙawanya a maɓoyarsu da ke Biya Cadde a yankin na Hirshabelle.

Rundunar Sojin ta Somalia ta ce har zuwa yanzu dakarun na ci gaba da luguden wuta a maɓoyar mayaƙan na al Shabaab.

A baya-bayan nan Sojojin Somalia na samun nasara kan mayaƙan al Shabaab inda ko a watan jiya ta hallaka da dama daga cikinsu kwanaki bayan Amurka ta musu luguden wuta da jiragen yaƙi.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp