Home General Tinubu ya nada sabon Daraktan hukumar NYSC

Tinubu ya nada sabon Daraktan hukumar NYSC

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu ya amince da nadin Birgediya Janar Kunle Nafiu matsayin sabon babban daraktan Hukumar yiwa kasa hidima ta NYSC.

Kafin nadin shine shugaban ma’aikatan Ofishin babban hafsan hafsoshin kasar Laftanar Janar Olufemi Oluyede, haka ya rike irin wannan mataki lokacin tsohon hafsan hafsoshin Marigayi Laftanar Janar Abiodun Lagbaja.

Birgediya Janar Nafiu guda ne cikin sojojin da suka fito daga cikin wadanda aka yaye a rukunin (47 regular Course) bangaren sojojin Atilare daga Kwalejin manyan sojoji ta Nijeriya da kuma Kwalejin yaki ta Amurka.

kafin zamansa shugaban ma’aikatan Ofishin babban hafsan hafsoshin kasar, ya rike mukamin daraktan ma’aikata na kwalejin yaki ta Nijeriya,

sabon babban daraktan hukumar ta NYSC ya fito daga garin Ileogbo, dake karamar hukumar Aiyedire a jihar Osun.

Nadin na Birgediya Janar Kunle Nafiu zai fara aiki nan take, wanda zai maye gurbin tsohon daraktan hukumar Birgediya Janar Yushau Ahmed.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp