Home General Tinubu ya nada sabon Daraktan hukumar NYSC

Tinubu ya nada sabon Daraktan hukumar NYSC

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu ya amince da nadin Birgediya Janar Kunle Nafiu matsayin sabon babban daraktan Hukumar yiwa kasa hidima ta NYSC.

Kafin nadin shine shugaban ma’aikatan Ofishin babban hafsan hafsoshin kasar Laftanar Janar Olufemi Oluyede, haka ya rike irin wannan mataki lokacin tsohon hafsan hafsoshin Marigayi Laftanar Janar Abiodun Lagbaja.

Birgediya Janar Nafiu guda ne cikin sojojin da suka fito daga cikin wadanda aka yaye a rukunin (47 regular Course) bangaren sojojin Atilare daga Kwalejin manyan sojoji ta Nijeriya da kuma Kwalejin yaki ta Amurka.

kafin zamansa shugaban ma’aikatan Ofishin babban hafsan hafsoshin kasar, ya rike mukamin daraktan ma’aikata na kwalejin yaki ta Nijeriya,

sabon babban daraktan hukumar ta NYSC ya fito daga garin Ileogbo, dake karamar hukumar Aiyedire a jihar Osun.

Nadin na Birgediya Janar Kunle Nafiu zai fara aiki nan take, wanda zai maye gurbin tsohon daraktan hukumar Birgediya Janar Yushau Ahmed.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp