Ƙungiyar kwadago ta Najeriya, NLC, ta yi kira ga gwamnatin tarayya da ta dakatar da yunƙurin ƙara kuɗin lantarki da masu amfani da layin A da B da C.
Wannan na kunshe cikin wata sanarwa da kungiyar ta fitar ranar lahadi, bayan wani taro da ta yi a jihar Adamawa dake arewa maso gabashin Nijeriya, inda ta bayyana rashin amincewar ta ta yunkurin na kara farashin wutar a kasar
“NLC ba ta amince da yunƙurin hukumar lantarki ta Najeriya NERC na ƙoƙarin sauya layin lantarki kwastomomi daga layin B da A da sunan haɓaka samun lantarki, alhali kuma yunƙuri ne kawai na ƙara wa mutane kuɗin wuta ba tare da sun shirya ba,” in ji sanarwar.
“A fili yake dai yanzu masu ƙarfi a ƙasar na ƙara jefa marasa ƙarfi cikin ƙunci ta hanyar ƙara kuɗin haraji da lantarki da sauransu a daidai lokacin da tattalin arzikin ƙasar ya tsaya cak.”
Ƙungiyar ta ƙara da cewa ba za ta lamunci ƙarin kuɗin wutar ba, inda ta yi barazanar shirya zanga-zanga idan har aka ƙara kuɗin lantarkin.











