Home General Zamu bawa hukumar Zane hadin Kai domin sake zaben kananan hukumomi-Fubara

Zamu bawa hukumar Zane hadin Kai domin sake zaben kananan hukumomi-Fubara

Gwamnan jihar Rivers, Siminalayi Fubara, ya tabbatar wa al’ummar jihar cewa gwamnatinsa za ta yi aiki da hukuncin kotun ƙolin ƙasar, bayan ta yi cikakken nazarin takardun hukuncin.

Yayin wani jawabi da ya gabatar wa ƴan jihar a ranar Lahadi, Mista Fubara ya ce gwamnatinsa za ta bai wa hukumar zaɓen jihar haɗin kai wajen sake shirya wani zaɓen ƙananan hukumomin, bayan kotun ta rushe wanda aka yi a shekarar da ta gabata

A ranar Juma’a kotun ƙolin ƙasar ta rushe zaɓen shugabannin ƙananan hukumomin jihar da aka gudanar ranar 5 ga watan Oktoban 2024.

Gwamnan ya kuma umarci duka shugabbanin ƙananan hukumomin su miƙa ragamar gudanar da ƙananan hukumomin ga daraktocin mulki na ƙananan hukukomin a gobe Litinin 3 ga wata.

Ya kuma bayyana aniyar naɗa shugabannin riƙo har zuwa lokacin da za a sake gudanar da wani sabon zaɓen.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp