Home General Akpabio da Natasha: Ku yi hankali kada kimar majalisa ta zube- Saraki

Akpabio da Natasha: Ku yi hankali kada kimar majalisa ta zube- Saraki

Tsohon shugaban majalisar dattawa, Sanata Bukola Saraki ya yi kira ga dukkan ɓangarorin shugaban majalisar dattawa, Sanata Godswill Akpabio da Sanata Natasha Akpoti da su iya bakinsu domin kare martabar majalisar.

A baya-bayan nan dai shugaban Majalisar Dattawan Sanata Godswill Akpabio ya riƙa samun saɓani da Sanata Natasha, lamarin da ya sa har Natasha ta shigar da shi ƙara a gaban kotu, kan zargin ɓata mata suna.

To sai dai tsohon Shugaban Majalisar Sanata Saraki ya ja kunne duka ɓangarorin don kauce wa zubar wa majalisar kima.

Cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa Facebook, Saraki ya ce abin da ya farun bai kamata ba, “wannan ya sa nake ganin ɓangarorin biyu da magoya bayansu na cikin majalisa da wajenta kowa ya iya bakinsa, kowa ya san tasirin da abin da yake aikatawa ko ya faɗa zai iya yi ga majalisar domin kare daraja da ƙimar da majalisa take da ita.”

Ya ce ya zama dole a bi dokar kundin tsarin mulki da dokokin majalisa wajen kawo ƙarshen wannan taƙaddama da ke tsakanin mutanen biyu.

“Sannan a yi komai a buɗe, ba tare da ba wa wani ɓangare fifiko ba. Abin da ya kamata a saka a gaba shi ne fito da gaskiya da kuma kare mutuncin majalisa wadda ita ce take da alhakin yin doka a ƙasa, saboda haka tana buƙatar a yi ƙoƙarin ba ta kariya da fito da mutuncinta.”

Ya ce a lokacin da yake shugaban majalisar, wani sanata ya zarge shi da fasaƙwaurin mota, “wanda hakan ya sa aka kafa kwamiti kuma a gaban ƴan jarida na kare kaina a gaban kwamitin.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp