Home General Akpabio da Natasha: Ku yi hankali kada kimar majalisa ta zube- Saraki

Akpabio da Natasha: Ku yi hankali kada kimar majalisa ta zube- Saraki

Tsohon shugaban majalisar dattawa, Sanata Bukola Saraki ya yi kira ga dukkan ɓangarorin shugaban majalisar dattawa, Sanata Godswill Akpabio da Sanata Natasha Akpoti da su iya bakinsu domin kare martabar majalisar.

A baya-bayan nan dai shugaban Majalisar Dattawan Sanata Godswill Akpabio ya riƙa samun saɓani da Sanata Natasha, lamarin da ya sa har Natasha ta shigar da shi ƙara a gaban kotu, kan zargin ɓata mata suna.

To sai dai tsohon Shugaban Majalisar Sanata Saraki ya ja kunne duka ɓangarorin don kauce wa zubar wa majalisar kima.

Cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa Facebook, Saraki ya ce abin da ya farun bai kamata ba, “wannan ya sa nake ganin ɓangarorin biyu da magoya bayansu na cikin majalisa da wajenta kowa ya iya bakinsa, kowa ya san tasirin da abin da yake aikatawa ko ya faɗa zai iya yi ga majalisar domin kare daraja da ƙimar da majalisa take da ita.”

Ya ce ya zama dole a bi dokar kundin tsarin mulki da dokokin majalisa wajen kawo ƙarshen wannan taƙaddama da ke tsakanin mutanen biyu.

“Sannan a yi komai a buɗe, ba tare da ba wa wani ɓangare fifiko ba. Abin da ya kamata a saka a gaba shi ne fito da gaskiya da kuma kare mutuncin majalisa wadda ita ce take da alhakin yin doka a ƙasa, saboda haka tana buƙatar a yi ƙoƙarin ba ta kariya da fito da mutuncinta.”

Ya ce a lokacin da yake shugaban majalisar, wani sanata ya zarge shi da fasaƙwaurin mota, “wanda hakan ya sa aka kafa kwamiti kuma a gaban ƴan jarida na kare kaina a gaban kwamitin.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp