Home General Tinubu ya yi alhinin rasuwar tsohon shugaban Namibia

Tinubu ya yi alhinin rasuwar tsohon shugaban Namibia

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya bayyana alhininsa kan rasuwar tsohon shugaban ƙasar Namibia, Dr. Sam Nujoma.

Tinubu wanda mataimakinsa Kashim Shettima ya wakilta a wajen jana’izar ban girman da aka yi wa marigarin ya bayyana shi a matsayin jarumin da ya ƙarfafa wa ƙasashen Afirka gwiwa wajen neman ƴancin kansu.

Yayin da yake jawabi a wajen jana’izar, Kashim Shettima ya ce ƙasashen Afirka ba za su manta irin gudunmawar da Mista Nujoma ya ba su wajen tabbatar da ƴancin kawunansu ba.

Najoma wanda shi ne shugaban Namibia na farko – ya rasu ne a ranar 8 ga watan Fabrairu, yana da shekara 95 a duniya, bayan fama da jinya a wani asibiti a Windhoek, babban birnin ƙasar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp