Home General An saka dokar taƙaice zirga-zirga a mazaɓar Sanata Natasha

An saka dokar taƙaice zirga-zirga a mazaɓar Sanata Natasha

Shugaban ƙaramar hukumar Okehi da ke jihar Kogi, Amoka Monday, ya ayyana dokar taƙaita zirga-zirga a yankin ƙaramar hukumar sakamakon fargabar ɓarkewar rikici saboda haramta tarukan siyasa da gwamnan jihar ya yi a ranar Litinin.

A watan sanarwa da shugaban ƙaramar hukumar ya sanya wa hannu wadda jaridar Punch ta rawaito, Amoka Monday ya ce dokar taƙaita zirga-zirgar dole ce domin samar da zaman lafiya a ƙaramar hukumar.

Wannan dai ya biyo bayan sanarwar da Sanata Natasha ta fitar tana mai nanata cewa za ta yi gangamin siyasa a ƙaramar hukumar duk da hanin da rundunar ƴansandan jihar ta yi mata.

A ranar Litinin ne gwamna Ododo ya haramta dukkan wani taron siyasa a jihar.

Magoya bayan Sanata Natasha dai sun ce za su yi wannan gangami ne domin nuna goyon baya ga wakiliyar tasu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp