Home General Na Sami tarbiyya bazan iya cin zarafin Mata ba – Akpabio

Na Sami tarbiyya bazan iya cin zarafin Mata ba – Akpabio

Shugaban Majalisar Dattawan Nijeriya Godswill Akpabio ya musanta zargin cin zarafi ta hanyar lalata da Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan ta yi a kansa.

Ya musanta zargin ne a ranar Laraba bayan majalisar ta koma aiki daga gajeren hutun da ta tafi.

Sanata Akpabio ya nuna rashin jin daɗinsa game da abubuwan da ke yawo a shafukan sada zumunta kan zargin da ake masa inda ya yi watsi da shi baki ɗaya.

“Ban taɓa cin zarafin wata mace ba. Na samu tarbiyya daga mahaifiyata, kuma ina girmama mata. An taɓa ba ni lambar yabo ta gwamnan da ya fi kyautata wa mata a Nijeriya,” kamar yadda Sanata Akpabio ya bayyana.

Bayan nan ne sai Sanata Natasha ta miƙe tsaye ta gabatar da korafi a kansa a hukumance a gaban majalisar bisa zarge-zargen da take masa.

A yayin da take gabatar da ƙorafin, ta zargi Akpabio da cin zarafi ta hanyar lalata da amfani da ƙarfin iko ba bisa ƙa’ida ba da kuma tauye mata haƙƙinta na gudanar da ayyukan majalisa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp