Home General An samu fashewar ɗaya daga cikin manyan layin bututu man Najeriya

An samu fashewar ɗaya daga cikin manyan layin bututu man Najeriya

An samu wata fashewa a ɗaya daga cikin manyan layin bututu man Najeriya, da ke garin Bodo na ƙaramar hukumar Gokana da ke jihar Rivers.

A cikin daren jiya Litinin ne dai aka samu fashewar a bututun TNP, da Najeriya ke amfani da shi wajen tura mai tashar mai ta Bonny da ke jihar ta Rivers.

Har zuwa safiyar Talatar nan, ɓangaren da aka samu fashewar na ci da wuta, lamarin da ya sanya bakin haraƙi turnuke sararin samaniya.

Kawo yanzu dai hukumomin ƙasar basu tantance abinda ya haifar da fashewar ba, duk da dai akwai barazanar da tsageran yankin suka yi a kwanan nan na kai wa cibiyoyin mai hari, sakamakon yadda a baya-bayan nan gwamnatin ƙasar taƙi tura wa jihar kuɗaɗenta na wata-wata, bisa rikicin siyasar jihar da ke faruwa tsakanin ɓangaren zartarwa da na dokoki.

Itama dai kakakin rundunar ƴan sandan jihar Grace Iringe-Koko, ta ce basu kammala tattara baranai ba don sanin haƙiƙanin abinda ya faru.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp