Home General Tinubu ya bayyana Vice Admiral Ibas matsayin Gwamnan Jihar Rivers na riko

Tinubu ya bayyana Vice Admiral Ibas matsayin Gwamnan Jihar Rivers na riko

Bola Ahned Tinubu

Shugaban Kasa Bola Ahmad Tunubu Ya sanya Dokar Ta baci a jihar Ribas sakamakon Rikici da yaki ci yaki cinyewa.

Bola ahmad Tunubu wanda yayi wani gajeren jawabi da Yammacin wanann rana a fadar Shugaban kasa, Yace abinda ke faruwa a jihar Ribas ba zai yiwu su bari ya cigaba da faruwa ba.

Saboda an gaza samun daidaito tsakanin gwamnan jihar Fubara da Majalisar Dokokin jihar tun bayan da kotun Koli ta yanke Hukunci.

Bola ahmad Tunubu ya kara da cewa Gwamnan jihar ya dauki matakin rushe Zauren majalisar kuma ya gaza gyarawa, wanda hakan yasa Yan majalisar Jihar suka gaza samun cikakken matsuguni da zasuyi aikinsu kamar yadda kundin tsarin Mulkin kasar nan ya tanadar.

Shugaban kasa bola Ahmad Tunubu ya sanar da Vice admiral Ibokette Ibas Mai ritaya a matsayin wanda zai kula da Tafiyar da jihar Ta Ribas

Tinubu yace ya samu rahotanni dake nuna Yadda Yan bindiga suka fara kai hare hare manyan bututun Manfetur wanda hakan barazana ne.

Kuma Gwamnan jihar Da Mataimakinsa basu zo sun sanar dani yanayin tsaro dake fuskantar Jihar ba, don haka a matsayina na Shugaban kasa wajibi nayi amfani da dokar kasa da ta bani dama wajen kare rayuka da dukiyoyin alumma wajen sanya dokar tabaci a jihar.

Ina sanar da Yan Nijeriya cewa daga yau na dakatar da Gwamnan jihar ribas da Mataimakinsa da kuma dukkan Yan Majalisar jihar har na tsawon watanni 6.

Shugaban kasa bola Ahmad Tunubu ya sanar da Vice admiral Ibokette Ibas Mai ritaya a matsayin wanda zai kula da Tafiyar da jihar Ta Ribas

Sai dai kuma bangaren Sharia na jihar zai cigaba da tafiyar da aikinsa kamar Yadda suka saba acewar Shugaban kasa Bola Ahmad Tunubu.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp