Home General Tinubu ya bayyana Vice Admiral Ibas matsayin Gwamnan Jihar Rivers na riko

Tinubu ya bayyana Vice Admiral Ibas matsayin Gwamnan Jihar Rivers na riko

Shugaban Kasa Bola Ahmad Tunubu Ya sanya Dokar Ta baci a jihar Ribas sakamakon Rikici da yaki ci yaki cinyewa.

Bola ahmad Tunubu wanda yayi wani gajeren jawabi da Yammacin wanann rana a fadar Shugaban kasa, Yace abinda ke faruwa a jihar Ribas ba zai yiwu su bari ya cigaba da faruwa ba.

Saboda an gaza samun daidaito tsakanin gwamnan jihar Fubara da Majalisar Dokokin jihar tun bayan da kotun Koli ta yanke Hukunci.

Bola ahmad Tunubu ya kara da cewa Gwamnan jihar ya dauki matakin rushe Zauren majalisar kuma ya gaza gyarawa, wanda hakan yasa Yan majalisar Jihar suka gaza samun cikakken matsuguni da zasuyi aikinsu kamar yadda kundin tsarin Mulkin kasar nan ya tanadar.

Shugaban kasa bola Ahmad Tunubu ya sanar da Vice admiral Ibokette Ibas Mai ritaya a matsayin wanda zai kula da Tafiyar da jihar Ta Ribas

Tinubu yace ya samu rahotanni dake nuna Yadda Yan bindiga suka fara kai hare hare manyan bututun Manfetur wanda hakan barazana ne.

Kuma Gwamnan jihar Da Mataimakinsa basu zo sun sanar dani yanayin tsaro dake fuskantar Jihar ba, don haka a matsayina na Shugaban kasa wajibi nayi amfani da dokar kasa da ta bani dama wajen kare rayuka da dukiyoyin alumma wajen sanya dokar tabaci a jihar.

Ina sanar da Yan Nijeriya cewa daga yau na dakatar da Gwamnan jihar ribas da Mataimakinsa da kuma dukkan Yan Majalisar jihar har na tsawon watanni 6.

Shugaban kasa bola Ahmad Tunubu ya sanar da Vice admiral Ibokette Ibas Mai ritaya a matsayin wanda zai kula da Tafiyar da jihar Ta Ribas

Sai dai kuma bangaren Sharia na jihar zai cigaba da tafiyar da aikinsa kamar Yadda suka saba acewar Shugaban kasa Bola Ahmad Tunubu.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp