Home General Mayaƙan Boko Haram sun hana gudanar da Sallar Juma’ar a Kamaru

Mayaƙan Boko Haram sun hana gudanar da Sallar Juma’ar a Kamaru

Rahotanni daga ƙasar Kamaru sun ce barazanar kai harin mayakan Boko Haram a garin Garwa ya sanya hana Sallar Juma’ar da aka saba gudanarwa a yau, abin da ya jefa jama’a cikin ruɗani.

Bayanan sun ce tun da safe aka yi ta yaɗa labarin shirin kai harin ƴanta’addan, waɗanda suka zafafa hare-harensu a ƴan kwanakin nan, wannan ta sa shugabanni ɗaukar matakin dakatar da Sallar Juma’ar domin kare lafiyar jama’a.

Cikin manyan Masallatan da aka rufe yau har da Masallachin tsohon shugaban ƙasa Ahmadu Ahidjo.

Wakilin RFI hausa a Garwa Rilwanou Shehu Ousmane ya tabbatar da aukuwar lamarin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp