Home General Tara jam’iyyu barkatai na dagula dimokuradiyya – Ganduje

Tara jam’iyyu barkatai na dagula dimokuradiyya – Ganduje

Shugaban jam’iyyar APC mai mulkin Najeriya, Abdullahi Umar Ganduje ya ce samun jam’iyyu barkatai na dagula tafiyar da gwamnnati a tsarin dimokraɗiyya.

Abdullahi Ganduje ya shaida hakan ne bayan ganawa da Shugaba Tinubu tare da wasu ƴan majalisar PDP da suka koma APC.

Shugaban, ya ce idan duka jam’iyyun siyasar ƙasar za su narke su koma APC, suna maraba da hakan.

”Yanzu idan ka duba ƙasar China tsarin jam’iyya guda suke bi, amma yau ƙasar China jagora ce a duniya wajen samar da ci gaban al’ummarsu”.

Ganduje ya ce idan ƴan Najeriya suka buƙaci komawa tsarin jam’iyyar guda, ba wanda zai yi faɗa da hakan.

Ƴanmajalisar Dattawan Najeriya uku na babbar jam’iyyar hamayya ta PDP daga jihar Kebbi za su sauya sheƙa zuwa jam’iyyar APC mai mulki, kamar yadda shugaban jam’iyyar APC na ƙasa ya tabbatar.

”Sanatocin jam’iyyar PDP daga jihar Kebbi a yau sun tabbatar wa shugaban ƙasa cewa sun fice daga jam’iyyarsu ta PDP tare da dawo jam’iyarmu ta APC”, in ji Ganduje.

Abdullahi Ganduje ya ce sanatocin uku za su bayyana wa majalisar dattawa matsayar tasu a mako mai zuwa kamar yadda kundin tsarin ƙasar ya tanadar.

Sanatocin uku sun haɗa da Sanata Adamu Aliero da Sanata Yahaya Abubakar Abdullahi da kuma Sanata Garba Maidoki.

A baya-bayan nan batun sauya sheƙa tsakanin manyan ƴansiyasa na ci gaba da ɗaukar hankali a ƙasar, bayan da wasu jiga-jigan jam’iyun hamayya ke komawa APC mai mulki.

Ko a makonnin baya ma gwamnan jihar Delta da tsohon gwamnan jihar, Ifeanyi Okowa – wanda shi ne ya yi wa PDP takarar mataimakin shugaban ƙasa a zaɓen 2023 – suka sanar da komawa APC.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp