Home General Tara jam’iyyu barkatai na dagula dimokuradiyya – Ganduje

Tara jam’iyyu barkatai na dagula dimokuradiyya – Ganduje

Shugaban jam’iyyar APC mai mulkin Najeriya, Abdullahi Umar Ganduje ya ce samun jam’iyyu barkatai na dagula tafiyar da gwamnnati a tsarin dimokraɗiyya.

Abdullahi Ganduje ya shaida hakan ne bayan ganawa da Shugaba Tinubu tare da wasu ƴan majalisar PDP da suka koma APC.

Shugaban, ya ce idan duka jam’iyyun siyasar ƙasar za su narke su koma APC, suna maraba da hakan.

”Yanzu idan ka duba ƙasar China tsarin jam’iyya guda suke bi, amma yau ƙasar China jagora ce a duniya wajen samar da ci gaban al’ummarsu”.

Ganduje ya ce idan ƴan Najeriya suka buƙaci komawa tsarin jam’iyyar guda, ba wanda zai yi faɗa da hakan.

Ƴanmajalisar Dattawan Najeriya uku na babbar jam’iyyar hamayya ta PDP daga jihar Kebbi za su sauya sheƙa zuwa jam’iyyar APC mai mulki, kamar yadda shugaban jam’iyyar APC na ƙasa ya tabbatar.

”Sanatocin jam’iyyar PDP daga jihar Kebbi a yau sun tabbatar wa shugaban ƙasa cewa sun fice daga jam’iyyarsu ta PDP tare da dawo jam’iyarmu ta APC”, in ji Ganduje.

Abdullahi Ganduje ya ce sanatocin uku za su bayyana wa majalisar dattawa matsayar tasu a mako mai zuwa kamar yadda kundin tsarin ƙasar ya tanadar.

Sanatocin uku sun haɗa da Sanata Adamu Aliero da Sanata Yahaya Abubakar Abdullahi da kuma Sanata Garba Maidoki.

A baya-bayan nan batun sauya sheƙa tsakanin manyan ƴansiyasa na ci gaba da ɗaukar hankali a ƙasar, bayan da wasu jiga-jigan jam’iyun hamayya ke komawa APC mai mulki.

Ko a makonnin baya ma gwamnan jihar Delta da tsohon gwamnan jihar, Ifeanyi Okowa – wanda shi ne ya yi wa PDP takarar mataimakin shugaban ƙasa a zaɓen 2023 – suka sanar da komawa APC.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp