Home Labarai Kano Ta Zama Cibiyar Bincike da Maganin Cututtuka na Zamani — Farfesa...

Kano Ta Zama Cibiyar Bincike da Maganin Cututtuka na Zamani — Farfesa Hamisu Salihu

Darakta Janar na Cibiyar Bincike Mai Zaman Kanta a Kano (KIRCT), Farfesa Hamisu Salihu, ya bayyana cewa sabbin fasahohin zamani da aka samar a bangaren lafiya sun sanya Jihar Kano ta fara taka rawa a matsayin cibiyar da za ta rika bayar da kulawa da magani na zamani a Najeriya.

Farfesa Salihu ya bayyana hakan ne a ranar Talata, yayin wata ziyarar duba wuraren aikin cibiyar da ke Kwanar Dawaki, a karamar hukumar Dawakin Kudu. Cibiyar na dauke da na’urori na zamani da ake amfani da su wajen bincike, nazari, gano cututtuka da sauran bangarorin da ke kara habaka a fannin kiwon lafiya.

A cewarsa, tare da sabuwar na’ura mai suna Next Gen 2000, cibiyar za ta taimaka wa marasa lafiya musamman masu fama da cutar Kansar Mama wajen gano ainihin nau’in cutar da ke damunsu. Wannan zai saukaka wajen samun maganin da ya dace da kowane nau’i na cutar, abin da zai karfafa damar warkar da marasa lafiya.

“Na’urar Next Gen 2000, wadda ita ce ta farko a Arewacin Najeriya, tana iya gano kwayar halittar kowanne irin kansa (cancer). Wannan bayani zai taimaka wajen gano ainihin nau’in cutar, kuma hakan zai ba mu damar daidaita magani daidai da nau’in kwayar cutar. Wannan ci gaba ne mai matukar amfani wajen ceton rayuka,” in ji Farfesa Salihu.

Ya kara da cewa, tare da na’urori irin su MI SEQ 1100+, B2 Solo – DNA, da kuma fasahar pharmacogenomics, jihar Kano ta yi watsi da tsoffin hanyoyin kula da cututtuka, ta kuma rungumi tsarin binciken ainihin tushen cuta da samar da magani da ya dace da kowanne mutum.

“Muna fatan ganin sabbin masu ba da kulawa a bangaren lafiya daga Kano, wadanda za su bayar da kulawa ta musamman ga kowane mutum. Lokacin amfani da irin magani daya ga kowa ya wuce. Tare da fasahar pharmacogenomics, za mu iya bayar da magani bisa bukatun kowane mutum,” in ji shi.

“Mun fara rage kashe kudade a bangaren lafiya, muna kara kudaden shiga ga jihar Kano, tare da inganta tsarin kiwon lafiya a jihar da kuma kasar baki daya,”

Har ila yau, ya bayyana cewa Hukumar Kula da Yaduwar Cututtuka ta Kasa (NCDC) da wasu hukumomin tarayya sun nuna sha’awarsu ga wannan cibiyar. Ana shirye-shirye don turo ma’aikatansu zuwa Kano domin koyon yadda ake amfani da fasahar genomics surveillance a kasar.

A yayin zagayen, an kuma bayyana cewa cibiyar na da asibiti na zamani da ke karbar marasa lafiya tare da basu kulawa ta musamman ta hanyar amfani da na’urori da kayan aiki na zamani.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp