Home Labarai Kano Ta Zama Cibiyar Bincike da Maganin Cututtuka na Zamani — Farfesa...

Kano Ta Zama Cibiyar Bincike da Maganin Cututtuka na Zamani — Farfesa Hamisu Salihu

Darakta Janar na Cibiyar Bincike Mai Zaman Kanta a Kano (KIRCT), Farfesa Hamisu Salihu, ya bayyana cewa sabbin fasahohin zamani da aka samar a bangaren lafiya sun sanya Jihar Kano ta fara taka rawa a matsayin cibiyar da za ta rika bayar da kulawa da magani na zamani a Najeriya.

Farfesa Salihu ya bayyana hakan ne a ranar Talata, yayin wata ziyarar duba wuraren aikin cibiyar da ke Kwanar Dawaki, a karamar hukumar Dawakin Kudu. Cibiyar na dauke da na’urori na zamani da ake amfani da su wajen bincike, nazari, gano cututtuka da sauran bangarorin da ke kara habaka a fannin kiwon lafiya.

A cewarsa, tare da sabuwar na’ura mai suna Next Gen 2000, cibiyar za ta taimaka wa marasa lafiya musamman masu fama da cutar Kansar Mama wajen gano ainihin nau’in cutar da ke damunsu. Wannan zai saukaka wajen samun maganin da ya dace da kowane nau’i na cutar, abin da zai karfafa damar warkar da marasa lafiya.

“Na’urar Next Gen 2000, wadda ita ce ta farko a Arewacin Najeriya, tana iya gano kwayar halittar kowanne irin kansa (cancer). Wannan bayani zai taimaka wajen gano ainihin nau’in cutar, kuma hakan zai ba mu damar daidaita magani daidai da nau’in kwayar cutar. Wannan ci gaba ne mai matukar amfani wajen ceton rayuka,” in ji Farfesa Salihu.

Ya kara da cewa, tare da na’urori irin su MI SEQ 1100+, B2 Solo – DNA, da kuma fasahar pharmacogenomics, jihar Kano ta yi watsi da tsoffin hanyoyin kula da cututtuka, ta kuma rungumi tsarin binciken ainihin tushen cuta da samar da magani da ya dace da kowanne mutum.

“Muna fatan ganin sabbin masu ba da kulawa a bangaren lafiya daga Kano, wadanda za su bayar da kulawa ta musamman ga kowane mutum. Lokacin amfani da irin magani daya ga kowa ya wuce. Tare da fasahar pharmacogenomics, za mu iya bayar da magani bisa bukatun kowane mutum,” in ji shi.

“Mun fara rage kashe kudade a bangaren lafiya, muna kara kudaden shiga ga jihar Kano, tare da inganta tsarin kiwon lafiya a jihar da kuma kasar baki daya,”

Har ila yau, ya bayyana cewa Hukumar Kula da Yaduwar Cututtuka ta Kasa (NCDC) da wasu hukumomin tarayya sun nuna sha’awarsu ga wannan cibiyar. Ana shirye-shirye don turo ma’aikatansu zuwa Kano domin koyon yadda ake amfani da fasahar genomics surveillance a kasar.

A yayin zagayen, an kuma bayyana cewa cibiyar na da asibiti na zamani da ke karbar marasa lafiya tare da basu kulawa ta musamman ta hanyar amfani da na’urori da kayan aiki na zamani.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp