Home Labarai Gwamnonin Arewacin Nijeriya sun yi Alhinin mutuwar sheik Dahiru Bauchi

Gwamnonin Arewacin Nijeriya sun yi Alhinin mutuwar sheik Dahiru Bauchi

Gwamnonin arewacin Najeriya sun nuna alhinin su bisa rasuwar jagoran ɗarikar Tijjaniyya a Najeriya Shiekh Dahiru Usman Bauchi wanda ya rasu a yau alhamis.

Gwamnan jihar Gombe Muhammad Inuwa Yahaya, wanda shi ne shugaban ƙungiyar ta gwamnonin jihohin arewa, ya bayyana Shehin a matsayin malamin da rayuwarsa da koyarwarsa suka taɓa rayukan miliyoyin mutane a tsawon shekaru.

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnatin jihar Gombe Uba Misili ya fitar, Gwamnan ya ce Sheikh Dahiru Bauchi ya sadaukar da rayuwarsa ta tsawon shekara 100 wajen yaɗa ilimin addinin musulunci, inda ya taimaka wajen koyar da karatun al Qurani da Hadisi da fiqihu da sauran karatuka.

Shugaban ƙungiyar gwamnonin Arewacin Najeriyar ya kuma ce malamin ya taka muhimiyyar rawa wajen samar da zaman lafiya,da juriya, da haɗin kai da kuma tarbiyya a tsawon rayuwarsa.

Ya kuma miƙa ta’aziyyar ɗaukacin gwamnonin arewacin Najeriya ga iyalan marigayin, da mabiya ɗariƙar Tijjaniyyah, da ma alummar musulmi kan gagarumin rashin da aka yi.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp