Home Labarai Najeriya da Turkiyya za su ƙarfafa alaƙa a ziyarar da Tinubu ke...

Najeriya da Turkiyya za su ƙarfafa alaƙa a ziyarar da Tinubu ke yi a ƙasar

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya samu kekkyawar tarba daga takwaransa na Turkiya Recep Tayib Erdogan, bayan sauƙarsa jiya a Ankara, a wata ziyarar aiki da nufin ƙarfafa alakar ƙasashen biyu, sai dai ɗan tuntuɓen da shugaban ya yi a lokacin da ake masa faretin ban girma ya haifar da cece-kuce a Najeriya.

A ziyarar wadda ita ce ta farko zuwa Turkiya tun bayan ɗarewarsa shugabancin Najeriya, shugaba Bola Tinubu ya ce, ƙasashen biyu sun sanya hannu kan yarjejeniyoyi da dama da suka haɗa da haɗin gwiwa kan horar da sojoji da tsara manufofin ƙasashen waje da manyan makarantu da sai sauransu.

Turkiya da Najeriya mai yawan jama’a a nahiyar Afirka  na da kyakkawar alaka diflomasiyya tun daga ranar 9 ga watan Nuwamba shekarar 1960.

Ko a baya-bayanan Najeriya ta ƙarfafa alakar tsaro da Turkiya, inda rudunar Sojan Sama ta Najeriya ta sayi jiragen sama marasa matuƙa da jiragen yaki masu saukar angula guda shida daga Türkiye.

Ana ɓangaren Turkiyya, kamfanonin ƙasar sun daɗe suna aiki a fannin gine-gine da makamashi da tufafi, da masana’antu a Najeriya, suna fitar da kayayyaki kamar ƙarafu da injina da abinci, yayin da suke shigo da ɗanyen mai da kayan noma.

Wani batu da ya ɗauki hankali yayin wannan ziyara, shine, ɗan tuntube da shugaba Tinubu ya yi har ya taɓa ƙasa, wanda bai hana shi ci gaba da gudanar da abin da ya kai shi ba, sai dai ƴan Najeriya sun ci gaba da tafka muhara a kafofin sada zumunta dangane da koshin lafiyarsa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp