Home Taska Gobara ta Tashi a Harabar Cibiyar Horar da Lauyoyi ta Najeriya

Gobara ta Tashi a Harabar Cibiyar Horar da Lauyoyi ta Najeriya

Gobara ta Tashi a Harabar Cibiyar Horar da Lauyoyi ta Najeriya 

 

An samu tashin gobara a daren ranar Laraba, 16 ga watan Fabrairu, a harabar cibiyar horar da lauyoyi ta Nigerian Law School dake kan titin Ozumba Mbadiwe a Victoria Island da ke jahar Legas.

Majiyoyin da suka zanta da ‘yan jarida sun bayyana cewa, lamarin ya haifar da tarzoma da tashin hankali a yankin.

TheCable ta ruwaito cewa, an nakalto daga majiya mai tushe a ranar Alhamis, 17 ga watan Fabrairu cewa gobarar ta tashi ne a sakamakon matsalar wutar lantarki da aka samu a cibiyar.

Duk da haka, an kashe gobarar cikin kankanin lokaci.

Majiyar ta ce:

“An samu tashin gobara jiya da daddare, amma nan take aka shawo kan ta. Gobarar ta faru ne sakamakon lalacewar wutar lantarki.”

A cewar Vanguard, kimanin mutane biyar da gobarar ta shafa sun kwanta a asibiti a halin yanzu.

Rahoton ya ce:

“Gobarar ta zo da wani kara. An samu turmutsutsu a dakin kwanan dalibai. Na ga wani dalibin da ya yi tsalle daga bene na farko inda gobarar ta tashi kusa da dakin karatu. Wasu daliban sun fice daga dakunansu a firgice.

“Akalla, mutane biyar sun samu munanan raunuka yayin da wata tsohuwa mace mai aikin shara ta samu gurdewa a yatsar kafa.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp