Home Taska Gobara ta Tashi a Harabar Cibiyar Horar da Lauyoyi ta Najeriya

Gobara ta Tashi a Harabar Cibiyar Horar da Lauyoyi ta Najeriya

Gobara ta Tashi a Harabar Cibiyar Horar da Lauyoyi ta Najeriya 

 

An samu tashin gobara a daren ranar Laraba, 16 ga watan Fabrairu, a harabar cibiyar horar da lauyoyi ta Nigerian Law School dake kan titin Ozumba Mbadiwe a Victoria Island da ke jahar Legas.

Majiyoyin da suka zanta da ‘yan jarida sun bayyana cewa, lamarin ya haifar da tarzoma da tashin hankali a yankin.

TheCable ta ruwaito cewa, an nakalto daga majiya mai tushe a ranar Alhamis, 17 ga watan Fabrairu cewa gobarar ta tashi ne a sakamakon matsalar wutar lantarki da aka samu a cibiyar.

Duk da haka, an kashe gobarar cikin kankanin lokaci.

Majiyar ta ce:

“An samu tashin gobara jiya da daddare, amma nan take aka shawo kan ta. Gobarar ta faru ne sakamakon lalacewar wutar lantarki.”

A cewar Vanguard, kimanin mutane biyar da gobarar ta shafa sun kwanta a asibiti a halin yanzu.

Rahoton ya ce:

“Gobarar ta zo da wani kara. An samu turmutsutsu a dakin kwanan dalibai. Na ga wani dalibin da ya yi tsalle daga bene na farko inda gobarar ta tashi kusa da dakin karatu. Wasu daliban sun fice daga dakunansu a firgice.

“Akalla, mutane biyar sun samu munanan raunuka yayin da wata tsohuwa mace mai aikin shara ta samu gurdewa a yatsar kafa.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp