Home Taska NITDA ta ba wa F.U.D Gudumawar Na’ura Mai Ƙwakwalwa Guda 150

NITDA ta ba wa F.U.D Gudumawar Na’ura Mai Ƙwakwalwa Guda 150

NITDA ta ba wa F.U.D Gudumawar Na’ura Mai Ƙwakwalwa Guda 150

Hukumar bunƙasa fasahar sadarwar zamani ta ƙasa, (NITDA), ƙarƙashin jagorancin Malam Kashif Inuwa Abdullahi, (CCIE), bisa kulawar ma’aikatar sadarwa da tattalin arziƙin zamani, ƙarƙashin jagorancin Farfesa Isah Ali Ibrahim Pantami, (FNCS, FBCS, FIIM), a wannan rana ta ba da gudunmawar na’ura mai ƙwaƙwalwa (Computers) jimillar guda (150) ga jami’ar gwamnatin tarayya da ke birnin Dutsen Jihar Jigawa, “Federal University Dutse”, (F.U.D).

A rahoton da jami’ar ta fitar ta cikin shafinta na sadarwa na (Facebook), sun bayyana cewa: daga cikin jimillar kwamfiyutocin, guda (100) waɗanda ake ɗorawa ne akan tebur, (Desktop Computers), samfurin kamfanin (Lenovo), sai kuma guda (50) na tafi da gidanka, (Laptops), samfurin ƙirar babban kamfanin nan na (HP).

Da ya ke jawabi a lokacin da ya ke gabatar da gudunmawar ga hukumar jami’ar, mai girma shugaban na (NITDA), Malam Kashif Inuwa, wanda Hannah Peter ya wakilta, ya bayyana cewa dalilin ba da gudunmawar shi ne domin a bunƙasa koyo da koyarwa na zamani a jami’ar.

A nasa martanin a ya yin da ya ke karɓan gudunmawar, muƙaddashin shugaban jami’ar, (VC), Farfesa Abdulkarim Sabo Muhammad, wanda shugaban tsangayar fasaha da kimiyyar zamantakewa, Farfesa Lawan Shu’aibu, ya wakilta, ya godewa shugaban na (NITDA), bisa wannan gagarumar gudunmawa wacce ya ce za ta taimaka wajen bunƙasa sha’anin koyo da koyarwa ta hanyar fasahar sadarwar zamani, tare kuma da cika babban burin shugaban jami’ar na ɗora ta akan turbar fasahar zamani.

Ƙarawa da cewa: “Shugaban (NITDA) mutum ne mai salo daban-daban, sannan mutum ne sahun farko wanda ya himmatu ka’in da na’in wajen samar da nagartattun ayyukan fasahar zamani a jami’o’in Nageriya domin ganin sun dace da (ƙarni na 21). Jami’armu ta (FUD) ta yi haɗin gwiwa akan abubuwa da dama tare da (NITDA), musamman a fannin harkar noma a ƙarƙashin cibiyarmu ta nazari da bincike kan noma, jami’armu ta na godiya ta musamman ga shugaban na (NITDA) akan wannan al’amari. Cewar shugaban (FUD), Farfesa Muhammad.

Lahadi, 20 ga watan Fabarairu, 2022.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp