Home Taska ‘Yan Bindiga Sun yi Garkuwa da Sarkin Pushit da ke Jahar Filato

‘Yan Bindiga Sun yi Garkuwa da Sarkin Pushit da ke Jahar Filato

‘Yan Bindiga Sun yi Garkuwa da Sarkin Pushit da ke Jahar Filato

Mutanen kauyen Pushit sun ga ta kansu yayin da ‘yan bindiga suka yi garkuwa da Mai garinsu.

A ranar Alhamsis aka ji ‘yan bindiga sun shigo Pushit, sun yi awon-gaba da Diket Gupiya a gidansa.

Jami’an ‘Yan Sanda da wasu mazauna wannan gari sun tabbatar da sace Mai martaba Diket Gupiya.

Plateau – Hankalin Bayin Allah ya tashi a karamar hukumar Mangu da ke jihar Filato bayan sace wani Basarake. Jaridar Punch ta fitar da wannan rahoto a yau.

Kamar yadda muka samu labari, ‘yan bindiga sun sace Mai martaba Diket Gupiya a Mangu.

Mai martaba Diket Gupiya shi ne mai rike da kasar Pushit. Daga wannan yanki a garin Mangu ne mataimakin gwamnan jihar Filato watau Sonny Tyoden ya fito.

Ana zargin wadannan ‘yan bindiga sun dauke Sarkin Pushit a fadarsa da ke kauyen Pushit a cikin daren ranar Alhamis din ta wuce, 24 ga watan Fubrairu 2022.

Wata majiya da shaidawa jaridar ta Punch cewa Diket Gupiya yana cikin gidansa yana kallon talabijin da kimanin karfe 9:00 na dare ne aka shigo masa daki.

Wadannan miyagu sun kawo hari, suka kuma yi nasarar yin awon gaba da Basaraken a jiya.
‘Yan bindigan sun yi gaba da Gupiya.Kawo yanzu ba a samu wani labari a game da inda aka kai shi ba. Ana tunanin za a nemi a biya kudin fansa kafin ya fito

. Tuni dai jami’an ‘yan sanda na jihar Filato ta bakin Ubah Ogaba sun bayyana cewa sun san da aukuwa lamarin, kuma an tura dakaru domin su ceto Gupiya.

Mun shiga uku – ‘Yan gari

Wani mazaunin yankin, Philip Moses ya shaidawa ‘yan jarida cewa an dauke Sarkin da ya taba neman canza sunan garinsa. Newsngr ta fitar da wannan rahoto.

“Abin takaici ya sake auka mana, an yi garkuwa da Cif Diket Gupiya, Mai garin mu a kasar Pushit a jiya Alhamis cikin dare.” – Philip Moses.

An kuma dauke Sarki

Ba wannan ne karon farko da aka ji irin wannan labari ba. Watanni biyu da suka wuce an ji cewa ‘yan bindiga sun sace Sarkin kasar Gundiri, Charles Mato.

Mai martaba Sum Pyem na Gundiri watau Charles Mato bai fito ba sai da aka biya kudin fansa. Wani ‘danuwan Sarkin ya bada labarin abin da ya wakana.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp