Home Taska ‘Yan Bindiga Sun yi Garkuwa da Sarkin Pushit da ke Jahar Filato

‘Yan Bindiga Sun yi Garkuwa da Sarkin Pushit da ke Jahar Filato

‘Yan Bindiga Sun yi Garkuwa da Sarkin Pushit da ke Jahar Filato

Mutanen kauyen Pushit sun ga ta kansu yayin da ‘yan bindiga suka yi garkuwa da Mai garinsu.

A ranar Alhamsis aka ji ‘yan bindiga sun shigo Pushit, sun yi awon-gaba da Diket Gupiya a gidansa.

Jami’an ‘Yan Sanda da wasu mazauna wannan gari sun tabbatar da sace Mai martaba Diket Gupiya.

Plateau – Hankalin Bayin Allah ya tashi a karamar hukumar Mangu da ke jihar Filato bayan sace wani Basarake. Jaridar Punch ta fitar da wannan rahoto a yau.

Kamar yadda muka samu labari, ‘yan bindiga sun sace Mai martaba Diket Gupiya a Mangu.

Mai martaba Diket Gupiya shi ne mai rike da kasar Pushit. Daga wannan yanki a garin Mangu ne mataimakin gwamnan jihar Filato watau Sonny Tyoden ya fito.

Ana zargin wadannan ‘yan bindiga sun dauke Sarkin Pushit a fadarsa da ke kauyen Pushit a cikin daren ranar Alhamis din ta wuce, 24 ga watan Fubrairu 2022.

Wata majiya da shaidawa jaridar ta Punch cewa Diket Gupiya yana cikin gidansa yana kallon talabijin da kimanin karfe 9:00 na dare ne aka shigo masa daki.

Wadannan miyagu sun kawo hari, suka kuma yi nasarar yin awon gaba da Basaraken a jiya.
‘Yan bindigan sun yi gaba da Gupiya.Kawo yanzu ba a samu wani labari a game da inda aka kai shi ba. Ana tunanin za a nemi a biya kudin fansa kafin ya fito

. Tuni dai jami’an ‘yan sanda na jihar Filato ta bakin Ubah Ogaba sun bayyana cewa sun san da aukuwa lamarin, kuma an tura dakaru domin su ceto Gupiya.

Mun shiga uku – ‘Yan gari

Wani mazaunin yankin, Philip Moses ya shaidawa ‘yan jarida cewa an dauke Sarkin da ya taba neman canza sunan garinsa. Newsngr ta fitar da wannan rahoto.

“Abin takaici ya sake auka mana, an yi garkuwa da Cif Diket Gupiya, Mai garin mu a kasar Pushit a jiya Alhamis cikin dare.” – Philip Moses.

An kuma dauke Sarki

Ba wannan ne karon farko da aka ji irin wannan labari ba. Watanni biyu da suka wuce an ji cewa ‘yan bindiga sun sace Sarkin kasar Gundiri, Charles Mato.

Mai martaba Sum Pyem na Gundiri watau Charles Mato bai fito ba sai da aka biya kudin fansa. Wani ‘danuwan Sarkin ya bada labarin abin da ya wakana.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp