Home Taska ‘Yan Ta’addan ISWAP Sun Kai Hari Karamar Hukumar Damboa da ke Jahar...

‘Yan Ta’addan ISWAP Sun Kai Hari Karamar Hukumar Damboa da ke Jahar Borno

‘Yan Ta’addan ISWAP Sun Kai Hari Karamar Hukumar Damboa da ke Jahar Borno

Yan ta’addan ISWAP sun kai hari kauyen Sabon-Gari da ke karamar hukumar Damboa ta jihar Borno.

Maharan sun halaka manoma 11 ciki harda mace a farmakin wanda suka kai a ranar Asabar.

Kauyen Sabon-Gari na a kimanin kilomita 125 daga garin Maiduguri, babbar birnin jihar Borno.

Borno – Daily Trust ta rahoto cewa mayakan kungiyar ta’addanci ta ISWAP ta kashe akalla manoma 11 a yayin wani farmaki da ta kai yankin kudancin jihar Borno.

An tattaro cewa ISWAP ta kai mamaya kauyen Sabon-Gari da ke karamar hukumar Damboa ta jihar a ranar Asabar, 27 ga watan Fabrairu.

Kauyen Sabon-Gari na a kimanin kilomita 125 daga garin Maiduguri, babbar birnin jihar.

A cewar wata majiya ta tsaro, an gano kimanin gawarwaki bakwai a ranar Asabar sannan aka sake samun wasu hudu a ranar Lahadi.

Rahoton ya kuma kawo cewa wata majiya ta kuma bayyana cewar harda mace a cikin mutanen da aka halaka.

Majiyar ta ce:

“Mun gano gawarwakin manoma 11, duk an harbe du ne sau da dama, an binnesu daidai da koyarwar addinin Islama.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp