Home Taska ‘Yan Ta’addan ISWAP Sun Kai Hari Karamar Hukumar Damboa da ke Jahar...

‘Yan Ta’addan ISWAP Sun Kai Hari Karamar Hukumar Damboa da ke Jahar Borno

‘Yan Ta’addan ISWAP Sun Kai Hari Karamar Hukumar Damboa da ke Jahar Borno

Yan ta’addan ISWAP sun kai hari kauyen Sabon-Gari da ke karamar hukumar Damboa ta jihar Borno.

Maharan sun halaka manoma 11 ciki harda mace a farmakin wanda suka kai a ranar Asabar.

Kauyen Sabon-Gari na a kimanin kilomita 125 daga garin Maiduguri, babbar birnin jihar Borno.

Borno – Daily Trust ta rahoto cewa mayakan kungiyar ta’addanci ta ISWAP ta kashe akalla manoma 11 a yayin wani farmaki da ta kai yankin kudancin jihar Borno.

An tattaro cewa ISWAP ta kai mamaya kauyen Sabon-Gari da ke karamar hukumar Damboa ta jihar a ranar Asabar, 27 ga watan Fabrairu.

Kauyen Sabon-Gari na a kimanin kilomita 125 daga garin Maiduguri, babbar birnin jihar.

A cewar wata majiya ta tsaro, an gano kimanin gawarwaki bakwai a ranar Asabar sannan aka sake samun wasu hudu a ranar Lahadi.

Rahoton ya kuma kawo cewa wata majiya ta kuma bayyana cewar harda mace a cikin mutanen da aka halaka.

Majiyar ta ce:

“Mun gano gawarwakin manoma 11, duk an harbe du ne sau da dama, an binnesu daidai da koyarwar addinin Islama.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp