Home Taska Hukumar Kwastam ta Kama Motar Dangote Makare da Shinkafar Waje 250

Hukumar Kwastam ta Kama Motar Dangote Makare da Shinkafar Waje 250

Hukumar Kwastam ta Kama Motar Dangote Makare da Shinkafar Waje 250

Hukumar kwastam a Najeriya ta yi nasarar cafke wata motar Dangote makare da shinkafar waje.

Hukumar ta bayyana kame motar dauke da buhuna 250 na haramtacciyar shinkafar ta kasar waje.

Hakazalika a wani yankin hukumar ta kame wasu haramtattun kayayakin da suka hada da fatan jaki, ganyen wiwi da sauransu.

Legas – Kwantrolla Janar na Kwastam, Team A Unit, Mohammed Yusuf, ya ce jami’an hukumar sun kwace wata motar babban Dangote makare da buhun shinkafa na kasar waje 250 da aka haramta shigo da su.

Yusuf ya bayyana hakan ne a ranar Alhamis a Ikeja, Legas, yayin taron manema labarai inda ya bada jawabin ayyukan da suka yi cikin makonni hudu a sassa daban-daban, The Punch ta ruwaito.

Ya bayyana cewa a cikin kayan da aka kwace akwai kwantena ta katako mai tsawon kafa 20; buhunan shinkafa masu nauyin 50kg guda 1000; taya na gwanjo guda 3,143; kunshin tufafin gwanjo 320; Buhun fatar jaki 44 da ganyen wiwi kilogiram 137.3.

“Ina farin cikin bayyana cewa cikin makonni hudu, tawaga ta Strike Force Team A, ta karbi N648,300,986 a matsayin haraji. Ta kuma kwace kaya da kudin harajinsu ya kai N373,629,700.

“Ina son in jadada cewa ba mu daukan aiki da wasa musamman aiki mai muhimmanci irin wannan. Masu fasakwabri da ke tunanin za su yi amfani da wannan damar su yi mummunan aikinsu za su sha mamaki,” in ji shi.

Mai magana da yawun sashin, Peter Duniya, ya tabbatar da cewa an kama motar kamfanin Dangote dauke da haramtatun kayan.

“Motar kamfanin Dangote na daya daga cikin kayayyakin da muka kama,” ya kara.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp