Home Taska Sojan Najeriya ya harbe Fararen Hula 3 Tare da Raunata Mutane 13

Sojan Najeriya ya harbe Fararen Hula 3 Tare da Raunata Mutane 13

Sojan Najeriya ya harbe Fararen Hula 3 Tare da Raunata Mutane 13

Wani sojan Najeriya da ake zargin yana tu’ammali da miyagun kwoyoyi ya harbe akalla fararen hula uku har lahira kuma ya raunata wasu mutum 13 yayin wani harbin mai-uwa-da-wabi da ya yi.

Wannan al’amarin ya auku ne a tsakiyar garin Mafa da ke jihar Borno a yankin arewa maso gabashin Najeriya.

Ganau sun ce cikin wadanda sojan ya halaka, akwai wata yarinya ‘yar shekara uku, sannan sauran mutum 13 na asibiti inda ake kula da su saboda raunukan da suka samu daga harbin da ya yi musu.

Wani rahoto ya ce sojan na cikin sojojin Najeriya da aka tura yankin domin yakar ‘yan kungiyar Boko Haram da na ISWAP.

Shaidu sun kuma ce an yi nasarar kwace bindigar daga hannun sojan kuma a halin yanzu yana hannun hukumomin soji.

Sai dai rundunar sojojin Najeriya ba ta ce uffan ba dangane da al’amarin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp