Home Taska Kotu a Babban Birnin Tarayya ta Gamsu da Nuna Adawa da ba...

Kotu a Babban Birnin Tarayya ta Gamsu da Nuna Adawa da ba da Belin Abba Kyari

Kotu a Babban Birnin Tarayya ta Gamsu da Nuna Adawa da ba da Belin Abba Kyari

 

Wata kotu a babban birnin tarayya ta yi zama, ta duba yiwuwar ba da belin DCP Abba Kyari da ake zargi da harkallar kwayoyi.

Kotun ta ce ta duba batutuwa da dama da hukumar NDLEA ta gabatar, inda tace ta gamsu da nuna adawa da ba da belin nasa.

Ana tuhumar Abba Kyari ne tare da wasu jami’ai bayan da bidiyo ya yadu da ke nuna suna kokarin kulla harkallar kwayoyi.

Abuja- Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta ki amincewa da bukatar neman belin da DCP Abba Kyari da mataimakin kwamishinan ‘yan sanda, Sunday J. Ubua suka shigar.

Idan baku manta ba ana tuhumarsu da laifukan da suka shafi harkallar muggan kwayoyi tare da wasu mutane biyar, The Nation ta ruwaito.

Mai shari’a Emeka Nwite, a wani hukunci da ya yanke a safiyar yau Litinin, ya ce masu gabatar da kara sun gabatar da isassun hujjoji a gaban kotu domin nuna kin amincewa da belin manyan jami’an ‘yan sandan biyu.

A maimakon haka, Mai shari’a Nwite ya ba da damar ci gaba da sauraron karar.

Wasu hotunan da gidan talabijin na TVC ya yada ya nuna lokacin da Abba Kyari tare da sauran wadanda ake zargi ke zaune a bakin kotu.

Karin bayani na nan tafe…

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp