Home Labarai ‘Yan Sanda a Jihar Zamfara Sun Sami Nasarar Kubutar da Mutane 39...

‘Yan Sanda a Jihar Zamfara Sun Sami Nasarar Kubutar da Mutane 39 da Hannun ‘Yan Bindiga

Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya ta sami nasarar kubutar da mutum 39 Mafi yawan su mata da kananan Yara da ‘Yan Bindiga sukayi garkuwa dasu a  jihar Zamfara.

Kakakin hukumar ‘Yan Sandan Jihar ta Zamfara Muhammad Shehu, ne ya bayyana hakan ta cikin wata sanarwa, inda yace wadanda aka kubutar din na cikin wadanda ‘Yan bindigar sukayi garkuwa dasu a kauyukan dake kananan hukumomin Maru da Bungudu.

“Wadanda aka kubutar sun hadarda Maza 8 Mata 15 cikin su harda masu shayarwa da kuma kananan yara 16” a cewar sa.

“Nasarar ta biyo bayan wani aikin share fage da Rundunar ‘Yan Sanda hadin Gwuiwa da Rundunar Soji suka gudanar a sansanin Dabar Magaji dake dajin Kadanya wanda ke tsakanin Kananan Hukumomin Kaura Namoda da Maradun.

Ya kara da cewa, “ ‘Yan sanda da hadin gwuiwar kungiyar likitocin Gwamnatin Jihar sun dukufa domin bawa wadanda aka ceto kulawa ta musamman, inda daga bisani kuma za’a mika su ga iyalan su, a cewar sa.

Rundunar ‘Yan Sandan ta ce ta sami nasarar kame wasu mutum 10 da ake zargi da aikata laifuka daban-daban daga cikin su akwai ‘yan haramtacciyar kungiyar ‘yan Sakai.

Yan Sakai kungiya ce ta ‘Yan banga da ke aiki a cikin yankin Arewa Maso Yamma, yawancin su mafarauta ne da ke aiki da Jami’an tsaro don kare Al’ummarsu daga ‘Yan fashin da ke kai farmaki a kauyuka da gonaki.

Daga cikin mutane goman da rundunar ta sami nasarar kamawa akwai mutum 3 da ake zargi da yin garkuwa da mutane 2 a unguwar fakon Idi dake talata mafarada kuma wasu mutane 2 da aka kama da laifin shiga gidaje da satar wayoyin hannu a Gusau babban birnin jihar ta Zamfara.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp