Home Labarai ‘Yan Sanda a Jihar Zamfara Sun Sami Nasarar Kubutar da Mutane 39...

‘Yan Sanda a Jihar Zamfara Sun Sami Nasarar Kubutar da Mutane 39 da Hannun ‘Yan Bindiga

Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya ta sami nasarar kubutar da mutum 39 Mafi yawan su mata da kananan Yara da ‘Yan Bindiga sukayi garkuwa dasu a  jihar Zamfara.

Kakakin hukumar ‘Yan Sandan Jihar ta Zamfara Muhammad Shehu, ne ya bayyana hakan ta cikin wata sanarwa, inda yace wadanda aka kubutar din na cikin wadanda ‘Yan bindigar sukayi garkuwa dasu a kauyukan dake kananan hukumomin Maru da Bungudu.

“Wadanda aka kubutar sun hadarda Maza 8 Mata 15 cikin su harda masu shayarwa da kuma kananan yara 16” a cewar sa.

“Nasarar ta biyo bayan wani aikin share fage da Rundunar ‘Yan Sanda hadin Gwuiwa da Rundunar Soji suka gudanar a sansanin Dabar Magaji dake dajin Kadanya wanda ke tsakanin Kananan Hukumomin Kaura Namoda da Maradun.

Ya kara da cewa, “ ‘Yan sanda da hadin gwuiwar kungiyar likitocin Gwamnatin Jihar sun dukufa domin bawa wadanda aka ceto kulawa ta musamman, inda daga bisani kuma za’a mika su ga iyalan su, a cewar sa.

Rundunar ‘Yan Sandan ta ce ta sami nasarar kame wasu mutum 10 da ake zargi da aikata laifuka daban-daban daga cikin su akwai ‘yan haramtacciyar kungiyar ‘yan Sakai.

Yan Sakai kungiya ce ta ‘Yan banga da ke aiki a cikin yankin Arewa Maso Yamma, yawancin su mafarauta ne da ke aiki da Jami’an tsaro don kare Al’ummarsu daga ‘Yan fashin da ke kai farmaki a kauyuka da gonaki.

Daga cikin mutane goman da rundunar ta sami nasarar kamawa akwai mutum 3 da ake zargi da yin garkuwa da mutane 2 a unguwar fakon Idi dake talata mafarada kuma wasu mutane 2 da aka kama da laifin shiga gidaje da satar wayoyin hannu a Gusau babban birnin jihar ta Zamfara.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp