Home Labarai Fadan Daba: Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Kano ta Haramta Tashe

Fadan Daba: Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Kano ta Haramta Tashe

Rundunar ‘yan sandan Jihar Kano ta haramta Al’adar nan ta tashe a Jihar.

Wannan na kunshe ne ta cikin wata sanarwa da Kakakin Rundunar ‘Yan Sandan Jihar SP Abdullahi Haruna Kiyawa ya fitar ranar Litinin.

“Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kano karkashin jagorancin kwamishinan ta CP Sama’ila Sha’aibu Dikko na sanar da al’ummar Jihar Kano cewa, a dakata da gudanar da Al’adar nan ta tashe, wadda ake yin ta daga 10 ga wata Azumin Ramadana, wannan ya biyo bayan fakewa da wasu bat a garin matasa ke yi da tashen suna fadan daba, kwacen waya da kuma ta’ammali da miyagun kwayoyi”.

SP Kiyawa ya yi kira ga iyaye da su tabbatar basu bar ‘Ya’yansu sun karya doka ba, domin kuwa duk wanda aka kama ya karya doka, ba shakka doka zatayi aiki akan shi.

Bisa al’ada, idan azumin watan Ramadan yakai kwanaki 10, akwai al’adar Tashe da kuma kidan gwauro da ake gudanarwa a kasar Hausa, wanda a wannan shekarar hukumar yan sanda ta jihar Kano, tace babu bukatar hakan, kuma tayi gargadi mai zafi ga duk wanda ya fito ya aiwatar da hakan.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp