Home Labarai Fadan Daba: Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Kano ta Haramta Tashe

Fadan Daba: Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Kano ta Haramta Tashe

Rundunar ‘yan sandan Jihar Kano ta haramta Al’adar nan ta tashe a Jihar.

Wannan na kunshe ne ta cikin wata sanarwa da Kakakin Rundunar ‘Yan Sandan Jihar SP Abdullahi Haruna Kiyawa ya fitar ranar Litinin.

“Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kano karkashin jagorancin kwamishinan ta CP Sama’ila Sha’aibu Dikko na sanar da al’ummar Jihar Kano cewa, a dakata da gudanar da Al’adar nan ta tashe, wadda ake yin ta daga 10 ga wata Azumin Ramadana, wannan ya biyo bayan fakewa da wasu bat a garin matasa ke yi da tashen suna fadan daba, kwacen waya da kuma ta’ammali da miyagun kwayoyi”.

SP Kiyawa ya yi kira ga iyaye da su tabbatar basu bar ‘Ya’yansu sun karya doka ba, domin kuwa duk wanda aka kama ya karya doka, ba shakka doka zatayi aiki akan shi.

Bisa al’ada, idan azumin watan Ramadan yakai kwanaki 10, akwai al’adar Tashe da kuma kidan gwauro da ake gudanarwa a kasar Hausa, wanda a wannan shekarar hukumar yan sanda ta jihar Kano, tace babu bukatar hakan, kuma tayi gargadi mai zafi ga duk wanda ya fito ya aiwatar da hakan.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp