Home Labarai TSARO: Dakarun MNJTF Sun Tarwatsa Maboyar Mayakan ISWAP

TSARO: Dakarun MNJTF Sun Tarwatsa Maboyar Mayakan ISWAP

Dakarun hadin gwuiwa na MNJTF sun yi Ruwan wuta kan sansanonin horas da mayakan kungiyar tada kayar baya ta Boko Haram tsagin ISWAP  da matsugunnan kwamandojin su a yankin Tafkin Chadi.

Wata majiyar liken asiri ta shaidawa PRNigeria cewa, dakarun sojin kakarshin jagorancin Rundunar Sojin Saman Nijar sun kai harin ne a ranar Alhamis, 14 ga Afrilun, 2022, a Tumbun Rego.

“Wani bayanin sirri ya nuna cewa wurin da aka kai harin ya zama wurin da manyan kwamandojin ISWAP ke zama, harin daya kai ga kawar da  wasu cikin kwamandojin da suka hada da Ibn Usman, Hani Abdullahi, Ababak Shuwa, Abu Jibrilla da Abu Ali.

“tare da hadin Gwuiwa jiragen yaki na Rundunar Sojin Saman Nijar, Jiragen sun kai hari a kusa da wuraren dake zama mafakar mayaka da iyalan ‘Yan Ta’addan.”

“A ranar 15 ga watan Afrilu, 2022 Rundunar Sojojin Nijeriya karkashin Operation Lake Sanity suka gudanar da aikin kawar da ‘Yan ta’addan, inda tuni suka kwace iko da yankuna da dama da ‘Yan ta’addan suke mamaye a dajin Sambisa tare da cigaba da kai musu hare-hare a dajin Tumbun.

“Hare-haren jiragen sama da kuma ayyukan sojojin kasa sun I sanadiyyar mutuwan ‘yan ta’adda da dama inda wasu da dama suka sami muggan raunika

PRNigeria Hausa

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp