Home Labarai TSARO: Dakarun MNJTF Sun Tarwatsa Maboyar Mayakan ISWAP

TSARO: Dakarun MNJTF Sun Tarwatsa Maboyar Mayakan ISWAP

Dakarun hadin gwuiwa na MNJTF sun yi Ruwan wuta kan sansanonin horas da mayakan kungiyar tada kayar baya ta Boko Haram tsagin ISWAP  da matsugunnan kwamandojin su a yankin Tafkin Chadi.

Wata majiyar liken asiri ta shaidawa PRNigeria cewa, dakarun sojin kakarshin jagorancin Rundunar Sojin Saman Nijar sun kai harin ne a ranar Alhamis, 14 ga Afrilun, 2022, a Tumbun Rego.

“Wani bayanin sirri ya nuna cewa wurin da aka kai harin ya zama wurin da manyan kwamandojin ISWAP ke zama, harin daya kai ga kawar da  wasu cikin kwamandojin da suka hada da Ibn Usman, Hani Abdullahi, Ababak Shuwa, Abu Jibrilla da Abu Ali.

“tare da hadin Gwuiwa jiragen yaki na Rundunar Sojin Saman Nijar, Jiragen sun kai hari a kusa da wuraren dake zama mafakar mayaka da iyalan ‘Yan Ta’addan.”

“A ranar 15 ga watan Afrilu, 2022 Rundunar Sojojin Nijeriya karkashin Operation Lake Sanity suka gudanar da aikin kawar da ‘Yan ta’addan, inda tuni suka kwace iko da yankuna da dama da ‘Yan ta’addan suke mamaye a dajin Sambisa tare da cigaba da kai musu hare-hare a dajin Tumbun.

“Hare-haren jiragen sama da kuma ayyukan sojojin kasa sun I sanadiyyar mutuwan ‘yan ta’adda da dama inda wasu da dama suka sami muggan raunika

PRNigeria Hausa

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp