Home Labarai TSARO: Dakarun MNJTF Sun Tarwatsa Maboyar Mayakan ISWAP

TSARO: Dakarun MNJTF Sun Tarwatsa Maboyar Mayakan ISWAP

Dakarun hadin gwuiwa na MNJTF sun yi Ruwan wuta kan sansanonin horas da mayakan kungiyar tada kayar baya ta Boko Haram tsagin ISWAP  da matsugunnan kwamandojin su a yankin Tafkin Chadi.

Wata majiyar liken asiri ta shaidawa PRNigeria cewa, dakarun sojin kakarshin jagorancin Rundunar Sojin Saman Nijar sun kai harin ne a ranar Alhamis, 14 ga Afrilun, 2022, a Tumbun Rego.

“Wani bayanin sirri ya nuna cewa wurin da aka kai harin ya zama wurin da manyan kwamandojin ISWAP ke zama, harin daya kai ga kawar da  wasu cikin kwamandojin da suka hada da Ibn Usman, Hani Abdullahi, Ababak Shuwa, Abu Jibrilla da Abu Ali.

“tare da hadin Gwuiwa jiragen yaki na Rundunar Sojin Saman Nijar, Jiragen sun kai hari a kusa da wuraren dake zama mafakar mayaka da iyalan ‘Yan Ta’addan.”

“A ranar 15 ga watan Afrilu, 2022 Rundunar Sojojin Nijeriya karkashin Operation Lake Sanity suka gudanar da aikin kawar da ‘Yan ta’addan, inda tuni suka kwace iko da yankuna da dama da ‘Yan ta’addan suke mamaye a dajin Sambisa tare da cigaba da kai musu hare-hare a dajin Tumbun.

“Hare-haren jiragen sama da kuma ayyukan sojojin kasa sun I sanadiyyar mutuwan ‘yan ta’adda da dama inda wasu da dama suka sami muggan raunika

PRNigeria Hausa

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp