Home SIYASA SIYASA: Kwankwaso Yayi Murabus

SIYASA: Kwankwaso Yayi Murabus

Kwamishinan Ma’aikatar Raya karkara ta Jihar Kano Dr Musa Iliyasu Kwankwaso ya ajiye mukamin sa na Kwamishina, sa’oi bayan gwamnan jihar ya bukaci hakan ga masu muradin tsayawa Takara cikin jami’an gwamnatin.

Hon. Musa Iliyasu Kwankwaso yace ya ajiye mukamin nasa ne domin yana da sha’awar yin takarar Dan Majalisar wakilai dake wakiltar Kananan Hukumomin Kura, Madobi da Garun Mallam a zauren majalisar wakilai a zabe mai zuwa, kamar yadda guda cikin hadiman sa Musa Dan Zariya ya shaidawa PRNigeria Hausa ta wayar tarho.

Tsohon Kwamishinan yace “Ina fatan Zan Zama Dan takarar Majalisar wakilai da zai wakilci Kananan Hukumomin Kura Madobi da Garun Mallam a jam’iyyar APC.

Tuni kwamishinan Ruwa na Jihar Kano Sadiq Wali yayi murabus daga kujerar sa, inda ya sayi Fom din takarar Gwaman jihar Kano a Jam’iyyar PDP.

Idan za’a iya tunawa a safiyar lahadi wani rahoto ya bayyana yadda gwamnan jihar Kano Dakta Abdullahi Umar Ganduje na bada Umarni ga Masu rike da mukamai a gwamnatin Kano dasu ajiye mukamansu Matukar suna da sha’awar tsayawa takara a zabe Mai Zuwa.

Umarnin daya yi dadai da sashe na 84 (12) na sabuwar dokar zabe da aka yiwa gyaran fuska.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp