Home SIYASA SIYASA: Kwankwaso Yayi Murabus

SIYASA: Kwankwaso Yayi Murabus

Kwamishinan Ma’aikatar Raya karkara ta Jihar Kano Dr Musa Iliyasu Kwankwaso ya ajiye mukamin sa na Kwamishina, sa’oi bayan gwamnan jihar ya bukaci hakan ga masu muradin tsayawa Takara cikin jami’an gwamnatin.

Hon. Musa Iliyasu Kwankwaso yace ya ajiye mukamin nasa ne domin yana da sha’awar yin takarar Dan Majalisar wakilai dake wakiltar Kananan Hukumomin Kura, Madobi da Garun Mallam a zauren majalisar wakilai a zabe mai zuwa, kamar yadda guda cikin hadiman sa Musa Dan Zariya ya shaidawa PRNigeria Hausa ta wayar tarho.

Tsohon Kwamishinan yace “Ina fatan Zan Zama Dan takarar Majalisar wakilai da zai wakilci Kananan Hukumomin Kura Madobi da Garun Mallam a jam’iyyar APC.

Tuni kwamishinan Ruwa na Jihar Kano Sadiq Wali yayi murabus daga kujerar sa, inda ya sayi Fom din takarar Gwaman jihar Kano a Jam’iyyar PDP.

Idan za’a iya tunawa a safiyar lahadi wani rahoto ya bayyana yadda gwamnan jihar Kano Dakta Abdullahi Umar Ganduje na bada Umarni ga Masu rike da mukamai a gwamnatin Kano dasu ajiye mukamansu Matukar suna da sha’awar tsayawa takara a zabe Mai Zuwa.

Umarnin daya yi dadai da sashe na 84 (12) na sabuwar dokar zabe da aka yiwa gyaran fuska.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp