Home SIYASA SIYASA: Kwankwaso Yayi Murabus

SIYASA: Kwankwaso Yayi Murabus

Kwamishinan Ma’aikatar Raya karkara ta Jihar Kano Dr Musa Iliyasu Kwankwaso ya ajiye mukamin sa na Kwamishina, sa’oi bayan gwamnan jihar ya bukaci hakan ga masu muradin tsayawa Takara cikin jami’an gwamnatin.

Hon. Musa Iliyasu Kwankwaso yace ya ajiye mukamin nasa ne domin yana da sha’awar yin takarar Dan Majalisar wakilai dake wakiltar Kananan Hukumomin Kura, Madobi da Garun Mallam a zauren majalisar wakilai a zabe mai zuwa, kamar yadda guda cikin hadiman sa Musa Dan Zariya ya shaidawa PRNigeria Hausa ta wayar tarho.

Tsohon Kwamishinan yace “Ina fatan Zan Zama Dan takarar Majalisar wakilai da zai wakilci Kananan Hukumomin Kura Madobi da Garun Mallam a jam’iyyar APC.

Tuni kwamishinan Ruwa na Jihar Kano Sadiq Wali yayi murabus daga kujerar sa, inda ya sayi Fom din takarar Gwaman jihar Kano a Jam’iyyar PDP.

Idan za’a iya tunawa a safiyar lahadi wani rahoto ya bayyana yadda gwamnan jihar Kano Dakta Abdullahi Umar Ganduje na bada Umarni ga Masu rike da mukamai a gwamnatin Kano dasu ajiye mukamansu Matukar suna da sha’awar tsayawa takara a zabe Mai Zuwa.

Umarnin daya yi dadai da sashe na 84 (12) na sabuwar dokar zabe da aka yiwa gyaran fuska.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp