Home Labarai TSARO: Mayakan ISWAP Sun Sauya Salon kai Hare-Hare a Yankin Arewa Maso...

TSARO: Mayakan ISWAP Sun Sauya Salon kai Hare-Hare a Yankin Arewa Maso Gabas

A wani yunkuri na kawo cikas ga nasarorin da Dakarun Sojin Nijeriya ke samu akan mayakan kungiyar tada kayar baya ta Boko Haram tsagin ISWAP, mayakan sun dauki salon dasa bama bamai a kan manyan hanyoyin dake yankin Arewa Maso Gabashin Nijeriya.

PRNigeria ta gano cewa mutane da dama sun rasa rayukan su sakamakon tarwatsewar wasu nakiyoyi mafi akasarin su kirara gida da ‘yan bindigar suka binne.

Wani bincike da PRNigeria ta gudanar Ya bayyana cewa yankunan da ‘Yan da ta’addan suka binne abubuwan fashewar sun hadar da Maiduguri, Damboa, Biu, Bama, Banki, Gwoza, Buni Yadi, Malam Fatori da Kukawa.

Majiyoyin jami’an tsaro sun shaida cewa za’a dauki tsawon lokaci kafin sojoji su kammala kunce nakiyoyin dake binne a karkashin kasar.

Ko a ‘yan tsakanin nan kwamandan Operation Hadin Kai Manjo Janar Christopher Musa, ya bayyana cewa gano bazuwar bama-baman babban kalubale ne a yakin da Rundunar ke yi da masu tayar da kayar baya a yankin.

Inda yace “Dakarun Sojin sai sun bincika ko ina kafin su gudanar da ayyukan su na kakkabe ‘yan ta’addan a ko ina, sannan sai sun sake bincikawa a hanyar su ta dawowa.

By PRNigeria

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp