Home Labarai TSARO: Mayakan ISWAP Sun Sauya Salon kai Hare-Hare a Yankin Arewa Maso...

TSARO: Mayakan ISWAP Sun Sauya Salon kai Hare-Hare a Yankin Arewa Maso Gabas

A wani yunkuri na kawo cikas ga nasarorin da Dakarun Sojin Nijeriya ke samu akan mayakan kungiyar tada kayar baya ta Boko Haram tsagin ISWAP, mayakan sun dauki salon dasa bama bamai a kan manyan hanyoyin dake yankin Arewa Maso Gabashin Nijeriya.

PRNigeria ta gano cewa mutane da dama sun rasa rayukan su sakamakon tarwatsewar wasu nakiyoyi mafi akasarin su kirara gida da ‘yan bindigar suka binne.

Wani bincike da PRNigeria ta gudanar Ya bayyana cewa yankunan da ‘Yan da ta’addan suka binne abubuwan fashewar sun hadar da Maiduguri, Damboa, Biu, Bama, Banki, Gwoza, Buni Yadi, Malam Fatori da Kukawa.

Majiyoyin jami’an tsaro sun shaida cewa za’a dauki tsawon lokaci kafin sojoji su kammala kunce nakiyoyin dake binne a karkashin kasar.

Ko a ‘yan tsakanin nan kwamandan Operation Hadin Kai Manjo Janar Christopher Musa, ya bayyana cewa gano bazuwar bama-baman babban kalubale ne a yakin da Rundunar ke yi da masu tayar da kayar baya a yankin.

Inda yace “Dakarun Sojin sai sun bincika ko ina kafin su gudanar da ayyukan su na kakkabe ‘yan ta’addan a ko ina, sannan sai sun sake bincikawa a hanyar su ta dawowa.

By PRNigeria

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp