Home Labarai TSARO: Mayakan ISWAP Sun Sauya Salon kai Hare-Hare a Yankin Arewa Maso...

TSARO: Mayakan ISWAP Sun Sauya Salon kai Hare-Hare a Yankin Arewa Maso Gabas

A wani yunkuri na kawo cikas ga nasarorin da Dakarun Sojin Nijeriya ke samu akan mayakan kungiyar tada kayar baya ta Boko Haram tsagin ISWAP, mayakan sun dauki salon dasa bama bamai a kan manyan hanyoyin dake yankin Arewa Maso Gabashin Nijeriya.

PRNigeria ta gano cewa mutane da dama sun rasa rayukan su sakamakon tarwatsewar wasu nakiyoyi mafi akasarin su kirara gida da ‘yan bindigar suka binne.

Wani bincike da PRNigeria ta gudanar Ya bayyana cewa yankunan da ‘Yan da ta’addan suka binne abubuwan fashewar sun hadar da Maiduguri, Damboa, Biu, Bama, Banki, Gwoza, Buni Yadi, Malam Fatori da Kukawa.

Majiyoyin jami’an tsaro sun shaida cewa za’a dauki tsawon lokaci kafin sojoji su kammala kunce nakiyoyin dake binne a karkashin kasar.

Ko a ‘yan tsakanin nan kwamandan Operation Hadin Kai Manjo Janar Christopher Musa, ya bayyana cewa gano bazuwar bama-baman babban kalubale ne a yakin da Rundunar ke yi da masu tayar da kayar baya a yankin.

Inda yace “Dakarun Sojin sai sun bincika ko ina kafin su gudanar da ayyukan su na kakkabe ‘yan ta’addan a ko ina, sannan sai sun sake bincikawa a hanyar su ta dawowa.

By PRNigeria

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp