Home Labarai LAFIYA: Gwamnatin Adamawa ta Sanar da Kawo Kashen Cutar Kwalara

LAFIYA: Gwamnatin Adamawa ta Sanar da Kawo Kashen Cutar Kwalara

Gwamnatin jihar Adamawa ta sanar da kawo karshen barkewar cutar kwalara data addabi jihar.

Wannan ya fito ne ta bakin Kwamishinan lafiya na jihar Farfesa Isa Abdullahi, yayin da yake ganawa da manema labarai ranar Alhamis a Yola Babban Birnin Jihar, inda yace cutar ta Kwalara ta barke ne a watan Yulin 2021, inda wata na gaba mutum 1,959 ake zargin sun kamu da cutar.

Ya zuwa ranar Alhamis, an sanar da kawo karshen barkewar cutar, wacce ta kama akalla mutum dubu biyu tayi sanadiyyar mutuwar mutane 55 a fadin jihar.

“Tun da  bamu sami rahoton bullar cutar kwalara ba, bayan sanya idanu da mukayi na tsawon makwannin Gwamanti da Abokan huldar ta, muna farin cikin sanar da cewa yanzu hakan babu cutar kwalara a jihar Adamawa.

Sai dai kwamishinan yace bayyana kawo karshen cutar ta kwalara, ba wai wata dama bace da al’umma zasu yi amfani da ita ba wajen shakatawa tare da yin watsi da dokokin da masana kiwon lafiya suka gindaya kan cutar.

Kawai wannan wata kofa ce ga mahukunta domin sake zage dantse wajen inganta shirye-shiryen magance dukkan cututtukan dake yaduwa, wajen samar da rigakafin su.

Daga bisani ya mika godiyar su ga Hukumar lafiya ta duniya WHO da kuma Asusu tallafawa kananan ya rana na Majalisar Dinkin Duniya UNICEF, da dukkan wadanda suka hada hannu da gwamnatin jihar tun daga watan Yuli har kawo yanzu da yawan masu kamuwa da cutar ya ragu matuka.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp