Home Labarai LAFIYA: Gwamnatin Adamawa ta Sanar da Kawo Kashen Cutar Kwalara

LAFIYA: Gwamnatin Adamawa ta Sanar da Kawo Kashen Cutar Kwalara

Gwamnatin jihar Adamawa ta sanar da kawo karshen barkewar cutar kwalara data addabi jihar.

Wannan ya fito ne ta bakin Kwamishinan lafiya na jihar Farfesa Isa Abdullahi, yayin da yake ganawa da manema labarai ranar Alhamis a Yola Babban Birnin Jihar, inda yace cutar ta Kwalara ta barke ne a watan Yulin 2021, inda wata na gaba mutum 1,959 ake zargin sun kamu da cutar.

Ya zuwa ranar Alhamis, an sanar da kawo karshen barkewar cutar, wacce ta kama akalla mutum dubu biyu tayi sanadiyyar mutuwar mutane 55 a fadin jihar.

“Tun da  bamu sami rahoton bullar cutar kwalara ba, bayan sanya idanu da mukayi na tsawon makwannin Gwamanti da Abokan huldar ta, muna farin cikin sanar da cewa yanzu hakan babu cutar kwalara a jihar Adamawa.

Sai dai kwamishinan yace bayyana kawo karshen cutar ta kwalara, ba wai wata dama bace da al’umma zasu yi amfani da ita ba wajen shakatawa tare da yin watsi da dokokin da masana kiwon lafiya suka gindaya kan cutar.

Kawai wannan wata kofa ce ga mahukunta domin sake zage dantse wajen inganta shirye-shiryen magance dukkan cututtukan dake yaduwa, wajen samar da rigakafin su.

Daga bisani ya mika godiyar su ga Hukumar lafiya ta duniya WHO da kuma Asusu tallafawa kananan ya rana na Majalisar Dinkin Duniya UNICEF, da dukkan wadanda suka hada hannu da gwamnatin jihar tun daga watan Yuli har kawo yanzu da yawan masu kamuwa da cutar ya ragu matuka.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp