Home Taska Manyan Hafsoshin Rundunar Kasa da na Sama Sun yi Bikin Karamar Sallah...

Manyan Hafsoshin Rundunar Kasa da na Sama Sun yi Bikin Karamar Sallah Tare da Dakarun su a Fagen Daga… Sun yi Alkawarin Inganta Walwalar Dakarun

Manyan Hafsoshin Rundunar Kasa da na Sama Sun yi Bikin Karamar Sallah Tare da Dakarun su a Fagen Daga… Sun yi Alkawarin Inganta Walwalar Dakarun

Babban hafsan sojin k’asan Najeriya Laftanar Janar Faruk Yahaya tare da takwaransa na rundunar sojin sama Air Marshal Isiaka Amao ranar litinin 2 ga Mayu 2022 sun yi bikin k’aramar sallah tare da dakarun fagen daga a Shelkwatar had’ad’d’iyar rundunar arewa maso gabas wato Operation HAD’IN KAI a Maiduguri.

Hafsoshin wad’anda suka gamsu da irin jajircewar dakarun, inda suka yi alk’awarin inganta walwalar su a yayin gudanar da bukukuwan k’aramar sallah.

A jawabin sa Babban hafsan sojin k’asan wanda tun da farko ya ziyarci dakarun da suka samu raunuka a Asibitin Runduna ta 7 inda ya yi alk’awarin samar da kula da lafiyar dakarun a gida Najeriya da kuma kasashen waje. Ya ce za’a koya masu sana’oin hannu domin kare su daga juyayin kwakwalwa.

A sak’on shi na fatan alheri, Babban hafsan sojin sama, ya yi kira ga dakarun had’ad’d’iyar rundunar da su kyautata had’in gwiwa wajen gudanar da ayyukan su. Ya kuma yi masu albishir na samar da sababbin kayayyakin aiki domin inganta yak’in sama.

Wakilin Mai Girma Gwamnan Jihar Borno, kuma mataimakin Gwamnan Jihar, Umar Usman Kadafur a sak’on sa na fatan alheri ya godewa dakarun had’ad’d’iyar rundunar arewa maso domin samar da zaman lafiya a jihar da yankin baki d’aya. Ya bayyana cewa nasarorin da aka samu ya nuna irin jajircewar rundunonin sojin na tabbatar da kawo k’arshen yak’in a yankin.

Birgediya Janar Onyema Nwachukwu
Daraktan Hulda da Jama’a na Rundunar Sojin Kasan Najeriya
2 Mayu 2022

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp