Home Taska Manyan Hafsoshin Rundunar Kasa da na Sama Sun yi Bikin Karamar Sallah...

Manyan Hafsoshin Rundunar Kasa da na Sama Sun yi Bikin Karamar Sallah Tare da Dakarun su a Fagen Daga… Sun yi Alkawarin Inganta Walwalar Dakarun

Manyan Hafsoshin Rundunar Kasa da na Sama Sun yi Bikin Karamar Sallah Tare da Dakarun su a Fagen Daga… Sun yi Alkawarin Inganta Walwalar Dakarun

Babban hafsan sojin k’asan Najeriya Laftanar Janar Faruk Yahaya tare da takwaransa na rundunar sojin sama Air Marshal Isiaka Amao ranar litinin 2 ga Mayu 2022 sun yi bikin k’aramar sallah tare da dakarun fagen daga a Shelkwatar had’ad’d’iyar rundunar arewa maso gabas wato Operation HAD’IN KAI a Maiduguri.

Hafsoshin wad’anda suka gamsu da irin jajircewar dakarun, inda suka yi alk’awarin inganta walwalar su a yayin gudanar da bukukuwan k’aramar sallah.

A jawabin sa Babban hafsan sojin k’asan wanda tun da farko ya ziyarci dakarun da suka samu raunuka a Asibitin Runduna ta 7 inda ya yi alk’awarin samar da kula da lafiyar dakarun a gida Najeriya da kuma kasashen waje. Ya ce za’a koya masu sana’oin hannu domin kare su daga juyayin kwakwalwa.

A sak’on shi na fatan alheri, Babban hafsan sojin sama, ya yi kira ga dakarun had’ad’d’iyar rundunar da su kyautata had’in gwiwa wajen gudanar da ayyukan su. Ya kuma yi masu albishir na samar da sababbin kayayyakin aiki domin inganta yak’in sama.

Wakilin Mai Girma Gwamnan Jihar Borno, kuma mataimakin Gwamnan Jihar, Umar Usman Kadafur a sak’on sa na fatan alheri ya godewa dakarun had’ad’d’iyar rundunar arewa maso domin samar da zaman lafiya a jihar da yankin baki d’aya. Ya bayyana cewa nasarorin da aka samu ya nuna irin jajircewar rundunonin sojin na tabbatar da kawo k’arshen yak’in a yankin.

Birgediya Janar Onyema Nwachukwu
Daraktan Hulda da Jama’a na Rundunar Sojin Kasan Najeriya
2 Mayu 2022

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp