Home Taska Shugaban NITDA ya Kai Ziyarar Gani da Ido Asibitin Gumel Tare da...

Shugaban NITDA ya Kai Ziyarar Gani da Ido Asibitin Gumel Tare da Ziyarar Girmamawa ga Mai Martaba Sarki

Kashifu Gumel

Shugaban NITDA ya Kai Ziyarar Gani da Ido Asibitin Gumel Tare da Ziyarar Girmamawa ga Mai Martaba Sarki

Mai girma shugaban hukumar (NITDA), Malam Kashif Inuwa Abdullahi, (CCIE), a ya yin da ya kai ziyara garin Gumel a jiya domin ganewa idonsa yadda aikin tiyatar ido, rabon maganin ciwon ido, da gilashin ƙara ƙarfin gani ya ke gudana a babbar Asibitin Garin na Gumel.

Aiki ne wanda gidauniyar ƙasar Qatar da haɗin gwiwar gidauniyarsa ta Malam Inuwa su ke gudanarwa kyauta ga al’ummar Jihar Jigawa.

A cikin jawabin da ya gabatar a ya yin hira da manema labarai a wurin, Malam Kashif Inuwa ya bayyana cewa aikin ya biyo bayan bincike ne da su ka gudanar su ka tabbatar da cewar Jihar Jigawa na sahun farko na Jihohin da ke fama da yawan masu lalurar ido, sannan kuma, duk mutum ɗaya zai kashe kuɗi kusan Naira dubu ɗari idan har zai je a yi masa aikin tiyatar idon, wannan dalili ya sanya gidauniyar tasa ta nemo wannan aiki daga gidauniyar ta ƙasar Qatar don a taimakawa al’umma kuma za a cigaba da yin wannan aiki a duk shiyoyin Jihar Jigawa duka.

Tunda farko gabanin duba aikin, shugaban hukumar ta (NITDA), ya fara da kai ziyarar girmamawa ga mai marba Sarkin Gumel, Alhaji Ahmad Muhammad Sani (CON), kana kuma ya samu rakiyar mai girma ɗan majalissar tarayya mai wakiltar ƙananan hukumomin; Gumel da Maigatari da Gagarawa da Suletankarkar, Onarabul Nazifi Sani Fulawa, da kuma mai girma shugaban ƙaramar hukumar ta Gumel, Onarabul Ahmad Rufa’i Gumel, da sauransu.

Ɗumbin al’umma waɗanda su ka amfana da shirin sun yi masa godiya da addu’o’i na fatan alkhairi bisa wannan aiki da ya samar dominsu.

Talata, 14 ga watan Yuni, 2022.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp