Home Taska Shugaban NITDA ya Kai Ziyarar Gani da Ido Asibitin Gumel Tare da...

Shugaban NITDA ya Kai Ziyarar Gani da Ido Asibitin Gumel Tare da Ziyarar Girmamawa ga Mai Martaba Sarki

Kashifu Gumel

Shugaban NITDA ya Kai Ziyarar Gani da Ido Asibitin Gumel Tare da Ziyarar Girmamawa ga Mai Martaba Sarki

Mai girma shugaban hukumar (NITDA), Malam Kashif Inuwa Abdullahi, (CCIE), a ya yin da ya kai ziyara garin Gumel a jiya domin ganewa idonsa yadda aikin tiyatar ido, rabon maganin ciwon ido, da gilashin ƙara ƙarfin gani ya ke gudana a babbar Asibitin Garin na Gumel.

Aiki ne wanda gidauniyar ƙasar Qatar da haɗin gwiwar gidauniyarsa ta Malam Inuwa su ke gudanarwa kyauta ga al’ummar Jihar Jigawa.

A cikin jawabin da ya gabatar a ya yin hira da manema labarai a wurin, Malam Kashif Inuwa ya bayyana cewa aikin ya biyo bayan bincike ne da su ka gudanar su ka tabbatar da cewar Jihar Jigawa na sahun farko na Jihohin da ke fama da yawan masu lalurar ido, sannan kuma, duk mutum ɗaya zai kashe kuɗi kusan Naira dubu ɗari idan har zai je a yi masa aikin tiyatar idon, wannan dalili ya sanya gidauniyar tasa ta nemo wannan aiki daga gidauniyar ta ƙasar Qatar don a taimakawa al’umma kuma za a cigaba da yin wannan aiki a duk shiyoyin Jihar Jigawa duka.

Tunda farko gabanin duba aikin, shugaban hukumar ta (NITDA), ya fara da kai ziyarar girmamawa ga mai marba Sarkin Gumel, Alhaji Ahmad Muhammad Sani (CON), kana kuma ya samu rakiyar mai girma ɗan majalissar tarayya mai wakiltar ƙananan hukumomin; Gumel da Maigatari da Gagarawa da Suletankarkar, Onarabul Nazifi Sani Fulawa, da kuma mai girma shugaban ƙaramar hukumar ta Gumel, Onarabul Ahmad Rufa’i Gumel, da sauransu.

Ɗumbin al’umma waɗanda su ka amfana da shirin sun yi masa godiya da addu’o’i na fatan alkhairi bisa wannan aiki da ya samar dominsu.

Talata, 14 ga watan Yuni, 2022.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp