Home General ‘Yan Bindiga Sun Hallaka Mutum 6 A Jihohin Kaduna Da Bauchi

‘Yan Bindiga Sun Hallaka Mutum 6 A Jihohin Kaduna Da Bauchi

Wasu mabanbanta hare-hare sunyi sanadiyyar mutuwar mutum 6 a jihohin Kaduna da Bauchi.

PRNigeria ta ruwaito cewa maharani da ake zrgi ‘yan bindiga ne suna halaka wasu manoma a gonakin su a kauyen Iyatawa dake karamar hukumar Igabi ta jihar Kaduna.

‘yan uwan wadanda lamarin ya rutsa dasu sunce mazauna kofar Jatau ne dake garin Zari’a, sun ce ‘yan  uwan nasu sun je gonakin nasu ne domin yin shuka, nan ne ‘yan bindigar suka haike musu, suka kuma halaka mutum 2 tare da yin garkuwa da  mutum 3.

Sun bayyana sunan wadanda ‘yan bindigar suka halaka da Alh. Mustapha lawan da Bello Lawal.

Sai dai an bayyana cewa ko a daminar Badi mahaifin wadanda aka halaka Alh. Lawal kofar Jatau ya tsallake rijiya da baya tare jin wasu muggana raunika a hannu ‘yan bindigar bayan da yaje gewaya gonar.

A wani labarin kuma wasu da ake zargin ‘yan bindiga sun kai hari garin Jamari Sabuwa dake  karamar hukumar Alkaleri ta jihar Bauchi, inda suka halaka mutum 4 tare da raunata mutum 3.

Shugaban karamar hukumar Alkaleri, Yusuf Garba, ya tabbatar da faruwar lamarin ranar Juma’a a garin Bauchi.

Yace ‘yan bindigar sun shiga garin ne inda sukayi garkuwa da Mai garin garin, bayan da Al’umma suka fahimci abinda ke faruwa ne suka tashi balli tare datarwatsa Shirin ‘yan bindiigar.

Shugaban karamar hukumarya tabbatar da cewa ‘yan bindigar sun fito daga cikin dajjin da yayi iyaka da jihohin Taraba, Gombe da kuma Plateau.

Wakilin mu ya rawaito mana cewa al’ummomin da lamarin ya shafa sun hadar da Tudun wada, Jada, Old Jamari, Sabuwa, Garin, Jauro Bano.

Wani mazaunin yankin Muhammad Usman ya shaidawa wakilin namu cewa ‘yan bindigar sun shiga garin ne da misalin karfe 11:45 na daren ranar Alhamis.

Kawo yanzu dai jami’an ‘yan sandan basu yi cikakken bayani kan wannan lamari ba, amma kakakin rundunar Muhammad Ahmad wakil yayi alkawarin tuntubar wakilin mu nan gaba kadan.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp