Home Labarai Kungiyar Ma’aikatan Jinya da Ungozoma (NANNM) ta Bukaci Adalci

Kungiyar Ma’aikatan Jinya da Ungozoma (NANNM) ta Bukaci Adalci

Kungiyar ma’aikatan jinya da Ungozoma ta kasa (NANNM), reshen birnin tarayya Abuja, ta bukaci a yi adalci bisa cin zarafin da akayi kan mambarta Abalu Marvis ta asibitin kasa dake Abuja.

Shugabar kungiyar, kwared Deborah Yusuf ce ta bayyana hakan yayin da take ganawa da manema labarai a ranar juma’a, inda tayi zargin cewa Dr. Atinko-Sunday Ikeya na asibiti ya afkawa Marvis yayin da take tsaka da lura da marasa lafiya.

Ta kara da cewa a ranar 13 ga watan yuni, Ikeyi yayi fatali da duk wata ka’ida ta aikin likitanci da ya kuma yi amfani da damar wajen cin zarafin ma’aikaciyar jinyar dake tsaka da aiki a matsayin abokiyar aikin sa.

Debora Yusuf tace, Jami’ar jinyar da likitan ya wulakanta, na tsaka da kula da wani mara lafiyar, likitan yace lallai sai ta bar wannan ta koma kan wanda ya uwace ta, wannan ya sanya har ta kai ga yaci zarafin ta.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp