Home Labarai Dan Bindiga 1 Ya Mutu ‘Yan Sanda Sun Kama 3 A Jihar...

Dan Bindiga 1 Ya Mutu ‘Yan Sanda Sun Kama 3 A Jihar Benue

Rundunar ‘Yan sandan Jihar Benue sun sami nasarar kame wasu da ake zargin na da hannu a kai harin garin Igama na karamar hukuma Okpokwu dake jihar.

ta cikin wata sanarwa da kakakin rundunar yan sandan jihar Catherine Anene ya fita a ranar Alhamis, yace wadanda ake zargin dai ya mutu ne sakamakon raunin harbi da ya samu a gwamzawar da jami’an ‘yan sandada gugun ‘yan bindigar.

Wakilin mu ya rawaito mana cewa maharan sun afka garin a yammacin ranar lahadi inda suka halaka mutum 15, daga bisani suka banka wuta a gidajen Al’ummar garin.

Ta cikin sanarwa rundunar ‘yan sandan ta tabbatar da jibge jami’anta hadin gwuiwa da sauran jami’an tsaro, domin bincika lungu da sako na dazukan dake yankin.

“A ranar 15 ga watan Yuni, misalin karfe 5 na safe, maharan dake makale a cikin daji, sun yi artabu da ‘yan sanda wanda ya kai ga an cafke Umar Nuhu, Dauda Alhaji, Musa Dako da Umaru Alhaji Sale.

“Daya daga cikin wadanda ake zargin mai suna Musa Dako ya samu raunuka kuma an kwantar da shi a Asibitin St. Mary’s dake Okpoga inda a karshe ya mutu.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp