Home Labarai CISA ta yaba da matakin da Sojoji suka dauka kan barayin man...

CISA ta yaba da matakin da Sojoji suka dauka kan barayin man fetur A Nijeriya

Wata kungiyar mai zaman kanta mai lakabin Citizen’s Initiative for Security Awareness (CISA) ta yaba da tsauraran matakan da sojojin Nijeriya ke dauka na dakile barnar da masu fasa bututun mai, da kuma masu fashin teku da sauran masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa.

Haka kuma kungiyar ta kalubalanci kiran da wasu kungiyoyi suka yi na sallamar babban hafsan hafsoshin Nijeriya Janar Lucky irabo kan kone jirgin da aka kama da laifin satar mai a yankin Neja Delta.

PRNigeria ta ruwaito cewa, a makon da ya gabata ne, rundunar sojin kasar ta bayar da Umarnin lalata wani jirgin Ruwan dakon mai da aka kama da laifin satar mai a wasu boyayyun wurare a yankin Nijer Delta.

Kamen jirgin ya zo ne a daidai lokacin da ‘yan Nijeriya ke cigaba da fahimtar yadda ake gano bututun mai da aka samar ba bisa ka’ida ba, wanda ake satar danyen mai da su wanda akwo yanzu ba’a bayyana wadanda ke da alhakin samar da bututun ba.

ba tare da bata lokaci ba sojoji sun kona jirgin ruwa da aka kama da laifin cin amanar kasa domin aika sakon gargadi ga masu ta’adar cin dinduniyar tattalin arzikin Nijeriya.

A cewar CDS, an kama kayan aikin tare da lalata su a matsayin wata hanya ta nuna yunkurin da sojoji suka yin a magance munanan laifuka da satar mai.

Ta cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannu kodinetan kungiyar na kasa, Chidi Omeje da sakataren ta, Olasunkanmi Ogunbodede mai take “suka ga kokarin dakarun sojojin domin dakile kokarin da suke na yaki da masu yiwa tattalin Arzikin kasa ta’annati CISA tayi Allah wadai da kakkausar murya kan kokarin da wasu mutane ke yi ta hanyar amfani da rahoton kona jirgin ruwa da aka kama da laifin satar mai a matsayin wukar kugu don yin gangami.

Kungiyar ta bayyana cewa, wadannan mutane kuma suna kokarin yin katsalan kan ayyukan babban hafsan Tsaron kasar, Janar Lucky Irabor, wanda suke kira da a tsige shi  saboda yunkurin sa na daukar matakan da suka dace.

PRNigeria

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp