Home DUNIYA Yunwa: Miliyoyin Mutane za su Sami Kansu a cikin Mawuyacin Hali a...

Yunwa: Miliyoyin Mutane za su Sami Kansu a cikin Mawuyacin Hali a Sudan ta Kudu

Majalisar Dinkin Duniya ta yi gargadin cewa kusan mutane miliyan takwas a Sudan ta Kudu, ko kashi biyu bisa uku na al’ummar kasar, za su fuskanci barazanar karancin abinci da tsananin yunwa.

Wani sabon rahoton da aka fitar ya bayyana cewa, yunwa da rashin abinci mai gina jiki na karuwa a yankunan da ambaliyar ruwa da fari da tashe-tashen hankula suka shafa a Sudan ta Kudu, kuma wasu al’ummomi na fuskantar barazanar yunwa matukar ba a ci gaba da gudanar da ayyukan jin kai ba.

Rahoton hadin gwiwa na Hukumar Abinci da Aikin Noma ta Majalisar Dinkin Duniya FAO, Asusun Kula da kananan yara na Majalisar Dinkin Duniya UNICEF, da Hukumar Abinci ta Duniya (WFP) sun ce adadin mutanen da ke fuskantar matsanancin karancin abinci da rashin abinci mai gina jiki ba a taba samun sa ba, wanda hakan ke nuni da cewa matsalar ta  wuce irin wacce aka gani lokacin shekarar 2013 da 2016.

Rahoton ya ce mutane miliyan 7.76 ne ke fuskantar barazanar karancin abinci a lokacin bazara daga Afrilu zuwa Yulin 2023, yayin da yara miliyan 1.4 za su yi fama da cutar tamowa.

Rahoton ya zargi rikice-rikice, rashin kyawun yanayin tattalin arziki, matsanancin dumamar yanayi, da hauhawar farashin abinci da man fetur, da kuma raguwar kudade don inganta ayyukan jin kai, shima ya kara dagula lamuran.

“Mun kasance cikin wani yanayi da ke neman daukin gaggawa na rigakafin yunwa domin guje wa mummunan sakamako, amma hakan da alama bam ai yuwu wa bane,” in ji Makena Walker, mukaddashin darektan WFP a Sudan ta Kudu.

Walker ya kara da cewa, Sudan ta Kudu na kan gaba wajen fuskantar matsalar sauyin yanayi, kuma a kowace rana, iyalai na rasa muhallansu, da dabbobi, da gonakinsu, saboda tsananin sauyin yanayi.

“Idan ba tare da taimakon abinci na jin kai ba, miliyoyin mutane za su sami kansu a cikin mawuyacin hali kuma ba za su iya samun abinci mai inganci da gina jiki ga iyakansu ba,” a ciwar Majalisar Dinkin Duniya

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp