Home Labarai Kamfanin Emirates ya soke zirga-zirga zuwa Nijeriya

Kamfanin Emirates ya soke zirga-zirga zuwa Nijeriya

Kamfanin sufurin jiragen sama na Emirates ya soke zirga-zirga zuwa Najeriya saboda kuɗaɗensa da ya ce gwamnatin ƙasar ta hana shi taɓawa.

Kamfanin na Daular Larabawa ya ƙara da cewa har yanzu bai samu kasonsa ba na dala miliyan 260 da Babban Bankin Najeriya (CBN) ya sakar wa kamfanonin ƙasar waje na kuɗin tikiti da suka sayar a Najeriyar.

A watan Satumba ne Emirates ya koma zirga-zirga a Najeriya bayan CBN ya sanar da sakin kuɗin, wanda wani ɓangare ne na fiye da dala miliyan 600 da kamfanonin jiragen ke son kwashewa zuwa ƙasashensu na asali.

“Har yanzu Emirates bai samu nasa kason ba daga cikin kuɗin da ya kamata ya kai gida,” a cewar sanarwar da ya fitar ranar Alhamis.

“Idan ba a kwashe kuɗin zuwa gida ba kuma ba tare da wani tsarin da zai tabbatar da cewa kuɗaɗen ba su ci gaba da taruwa ba…ba za mu iya ci gaba da aiki ba balle ma zirga-zirgarmu zuwa Najeriya.”

Ko da yake dai ana kallon wannan mataki na kamfanin matsayin wani bangare na rashin jituwar dake tsakanin daular larabawan da Nijeriyar duk da kamfanin bai fito karara ya bayyana hakan ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp