Home Labarai Kotu ta Tura Masu Tiktok 2 Gidan Yari Saboda Sukar Gwamna Ganduje

Kotu ta Tura Masu Tiktok 2 Gidan Yari Saboda Sukar Gwamna Ganduje

Kotu ta Tura Masu Tiktok 2 Gidan Yari Saboda Sukar Gwamna Ganduje

 

An gurfanar da wasu masu sana’ar TikTok guda biyu Mubarak Muhammad (Uniquepikin) da Nazifi Muhammad a gidan yari bisa zargin bata sunan gwamnan Kano Abdullahi Ganduje a daya daga cikin wasannin barkwanci da suka yi.

Rahotanni sun bayyana cewa, ‘yan biyun sun yi zagon kasa inda suka nuna gwamnan jihar Kano, Abdullahi Ganduje a matsayin dan siyasa mai cin hanci da rashawa, wanda ya siyar da duk wani fili na jama’a a jihar.

‘Yan sanda sun gurfanar da su a gaban kotun majistare mai lamba 58, Nomansland, karkashin jagorancin Alkalin Kotun, Aminu Gabari.

Lokacin da aka karanta musu tuhume-tuhumen, TikTokers biyu sun amsa laifin da ake tuhumar su da su na hada baki da kuma bata sunan gwamnan.

Don haka alkalin kotun ya bayar da umarnin a ci gaba da tsare su a gidan yari tare da dage sauraron karar zuwa ranar 7 ga watan Nuwamba domin yanke hukunci.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp