Home General Ganduje ya sanya hannu kan kasafin kudin 2023

Ganduje ya sanya hannu kan kasafin kudin 2023

Gwamnan Jihar Kano Dr Abdullahi Umar Ganduje ya rattaba hannu a Kasafin kudin Shekara ta 2023 wanda Majalisar Dokoki ta Jihar Kano ta Amince da shi.
Gwamnan ya Sanya hannun ne yayin taron Majalisar Zartarwar ta Jihar Kano wanda ya gudana a dakin taron majalisar dake gidan gwamnatin jiha.
Gwamna Ganduje ya yabawa yan majalisar bisa yadda sukai aikin kasafin kudin ba tare da bata lokaci ba, Wanda hakan zai baiwa Gwamnatin damar fara amfani da kasafin kudin a farkon sabuwar Shekara tunda ya Zama doka.
Gwamnan Ganduje yace bai yi mamakin yadda yan Majalisar suka kammala aikin nasu da wuri ba, Inda yace zai tabbatar an yi aikin da kasafin kudin kamar yadda majalisar ta amince da shi.
Ganduje ya yi alkawarin Cigaba da baiwa Majalisar yancin cin gashin kanta, ba tare da tsoma baki a harkokin aikin Majalisar ba.
Ya Kuma yaba da yadda Majalisar ta Gudanar da taron Jin ra’ayoyin al’umma akan kasafin, Inda ya bada tabbacin Kasafin kudin zai fi mai da hankali wajen kammala aiyukan da suka fara don gudun barin bashi mai yawa ga gwamnati mai zuwa, Inda yace kasafin kudin ya samu kari daga Sama da Naira Biliyan 23.
tun da fari Shugaban Majalisar Dokoki ta Jihar Kano Hamisu Ibrahim Chidari yace sun Sami nasarar kammala aikin nasu ne akan lokaci Saboda yadda Gwamnan ya gabatar musu da daftarin Kasafin akan Lokaci.
Chidari yace Kuma dukkanin Shugabannin Ma’aikatu da Hukumomin Gwamnatin Jihar Kano sun bayar da duk wani hadin Kai ga kwamitocin Majalisar wanda hakan ya taimaka wajen Samun nasarar aikin kasafin kudin kamar yadda doka ta basu dama.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp