Home General Ganduje ya sanya hannu kan kasafin kudin 2023

Ganduje ya sanya hannu kan kasafin kudin 2023

Gwamnan Jihar Kano Dr Abdullahi Umar Ganduje ya rattaba hannu a Kasafin kudin Shekara ta 2023 wanda Majalisar Dokoki ta Jihar Kano ta Amince da shi.
Gwamnan ya Sanya hannun ne yayin taron Majalisar Zartarwar ta Jihar Kano wanda ya gudana a dakin taron majalisar dake gidan gwamnatin jiha.
Gwamna Ganduje ya yabawa yan majalisar bisa yadda sukai aikin kasafin kudin ba tare da bata lokaci ba, Wanda hakan zai baiwa Gwamnatin damar fara amfani da kasafin kudin a farkon sabuwar Shekara tunda ya Zama doka.
Gwamnan Ganduje yace bai yi mamakin yadda yan Majalisar suka kammala aikin nasu da wuri ba, Inda yace zai tabbatar an yi aikin da kasafin kudin kamar yadda majalisar ta amince da shi.
Ganduje ya yi alkawarin Cigaba da baiwa Majalisar yancin cin gashin kanta, ba tare da tsoma baki a harkokin aikin Majalisar ba.
Ya Kuma yaba da yadda Majalisar ta Gudanar da taron Jin ra’ayoyin al’umma akan kasafin, Inda ya bada tabbacin Kasafin kudin zai fi mai da hankali wajen kammala aiyukan da suka fara don gudun barin bashi mai yawa ga gwamnati mai zuwa, Inda yace kasafin kudin ya samu kari daga Sama da Naira Biliyan 23.
tun da fari Shugaban Majalisar Dokoki ta Jihar Kano Hamisu Ibrahim Chidari yace sun Sami nasarar kammala aikin nasu ne akan lokaci Saboda yadda Gwamnan ya gabatar musu da daftarin Kasafin akan Lokaci.
Chidari yace Kuma dukkanin Shugabannin Ma’aikatu da Hukumomin Gwamnatin Jihar Kano sun bayar da duk wani hadin Kai ga kwamitocin Majalisar wanda hakan ya taimaka wajen Samun nasarar aikin kasafin kudin kamar yadda doka ta basu dama.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp