Home General Babban Sifeton ‘yan sandan Najeriya Usman Alkali Baba, ya gana da gwamnan...

Babban Sifeton ‘yan sandan Najeriya Usman Alkali Baba, ya gana da gwamnan jihar Legas Babajide Sanwo-Olu

Babban Sifeton ‘yan sandan Najeriya Usman Alkali Baba, ya gana da gwamnan jihar Legas Babajide Sanwo-Olu a shelkwatar hukumar ‘yan sandan ƙasar da ke Abuja babban birnin ƙasar, domin tattauna wasu batutuwa ciki har da batun yin adalci ga lauyar nan da wani jami’an ɗan sanda ya harbe a birnin Legas ranar Kirsimeti.

A cikin wata sanarwa da rundunar ‘yan sandan ta fitar mai dauke da sa hannun jami’in hulda da jama’a na rundunar ya ce babban sifeton ‘yan sandan, ya jadda cewa za a gudanar da cikakken bincike tare da alƙawarin yin adalci game da batun, yana mai cewa hukumar na aiki kafaɗa-da-kafaɗa da ofishin babban lauyan gwamnatin jihar Legas domin tabbatar da an gurfanar da wanda ke da hannu a gaban kotu.

A nasa ɓangare gwamnan jihar Legas ɗin ya alkawarta taimaka wa rundunar ‘yan sandan domin ganin cewa an yi adalci game da binciken kisan lauyar.

Tuni dai babban Sifeton ‘yan Sandan ƙasar ya bayar da umarnin dakatar da jami’in ɗan sandan da ya harbe tare da kashe lauyar mai suna Omobolanle Raheem a birnin Legas.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp