Home General Babban Sifeton ‘yan sandan Najeriya Usman Alkali Baba, ya gana da gwamnan...

Babban Sifeton ‘yan sandan Najeriya Usman Alkali Baba, ya gana da gwamnan jihar Legas Babajide Sanwo-Olu

Babban Sifeton ‘yan sandan Najeriya Usman Alkali Baba, ya gana da gwamnan jihar Legas Babajide Sanwo-Olu a shelkwatar hukumar ‘yan sandan ƙasar da ke Abuja babban birnin ƙasar, domin tattauna wasu batutuwa ciki har da batun yin adalci ga lauyar nan da wani jami’an ɗan sanda ya harbe a birnin Legas ranar Kirsimeti.

A cikin wata sanarwa da rundunar ‘yan sandan ta fitar mai dauke da sa hannun jami’in hulda da jama’a na rundunar ya ce babban sifeton ‘yan sandan, ya jadda cewa za a gudanar da cikakken bincike tare da alƙawarin yin adalci game da batun, yana mai cewa hukumar na aiki kafaɗa-da-kafaɗa da ofishin babban lauyan gwamnatin jihar Legas domin tabbatar da an gurfanar da wanda ke da hannu a gaban kotu.

A nasa ɓangare gwamnan jihar Legas ɗin ya alkawarta taimaka wa rundunar ‘yan sandan domin ganin cewa an yi adalci game da binciken kisan lauyar.

Tuni dai babban Sifeton ‘yan Sandan ƙasar ya bayar da umarnin dakatar da jami’in ɗan sandan da ya harbe tare da kashe lauyar mai suna Omobolanle Raheem a birnin Legas.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp