Home General Hukumar EFCC, ta bude kofa ga masu sha’awar sayan wasu kaddarorin gidade...

Hukumar EFCC, ta bude kofa ga masu sha’awar sayan wasu kaddarorin gidade da filaye 160 a kasar

Hukumar yaki da masu yiwa tattalin arzikin Nijeriya zagon kasa EFCC, ta bude kofa ga masu sha’awar sayan wasu kaddarorin gidade da filaye 160 a jahohin kasar 12 da aka kwace daga wajen wadanda aka zarga da cin hanci da rashawa.
Mai magana da yawun hukumar ta EFCC Wilson Uwujaren ne ya tabbatar da hakan a wata sanarwa da ya fitar a Abuja, babban birnin kasar.
Tuni dai wasu suka fara kiran gudanar da bincike wajen gano sahihancin kudaden wadanda za’a sake saida wa irin wadan nan kaddarori.
A bayan bayan nan ne rahotanni daga Najeriya ke cewa EFCC za ta yi gwanjon gidaje da filaye 144 da aka kwace a fadin kasar, inda jihohin Legas, Abuja da kuma Jihar Ribas ke kan gaba.
Kakakin EFCC ya bayyana cewa daga cikin kadadrorin, akwai gidaje 24 da ke rukunin gidaje na Banana Island, sai 21 a Thornburn, Yaba, duka a Legas,sai kuma 6 na a Court Estate da ke birnin Fatakwal.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp