Home General Hukumar EFCC, ta bude kofa ga masu sha’awar sayan wasu kaddarorin gidade...

Hukumar EFCC, ta bude kofa ga masu sha’awar sayan wasu kaddarorin gidade da filaye 160 a kasar

Hukumar yaki da masu yiwa tattalin arzikin Nijeriya zagon kasa EFCC, ta bude kofa ga masu sha’awar sayan wasu kaddarorin gidade da filaye 160 a jahohin kasar 12 da aka kwace daga wajen wadanda aka zarga da cin hanci da rashawa.
Mai magana da yawun hukumar ta EFCC Wilson Uwujaren ne ya tabbatar da hakan a wata sanarwa da ya fitar a Abuja, babban birnin kasar.
Tuni dai wasu suka fara kiran gudanar da bincike wajen gano sahihancin kudaden wadanda za’a sake saida wa irin wadan nan kaddarori.
A bayan bayan nan ne rahotanni daga Najeriya ke cewa EFCC za ta yi gwanjon gidaje da filaye 144 da aka kwace a fadin kasar, inda jihohin Legas, Abuja da kuma Jihar Ribas ke kan gaba.
Kakakin EFCC ya bayyana cewa daga cikin kadadrorin, akwai gidaje 24 da ke rukunin gidaje na Banana Island, sai 21 a Thornburn, Yaba, duka a Legas,sai kuma 6 na a Court Estate da ke birnin Fatakwal.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp