Home General Gwamnatin Jihar Kano Zata samar da Sabuwar Kwalejin koyar da harkokin Lafiya

Gwamnatin Jihar Kano Zata samar da Sabuwar Kwalejin koyar da harkokin Lafiya

Gwamnan jihar kano Dr Abdullahi Umar ya kaddamar da wani kwamiti da zai duba tare da yadda za’a samar da wata sabuwar Kwalegin koyar da harkokin kiwon lafiya domin magance matsalolin rashin Likitoci a kano da ma Nigeria baki daya.
Gwamna Ganduje ya kaddamar da kwamitin ne Mai mutane 19 yayin taron majalisar zartarwar ta jiha na wannnan makon wanda ya gudana a gidan gwamnatin jihar kano.
Ganduje ya bukaci yan kwamitin da su zage damtse wajen sauke nauyin da aka dora musu akan lokaci duba da muhimmanci da yadda al’ummar jihar kano ke bukatar Kwalegin saboda karacin jami’an lafiya da ake fama da su.
Ya ce an dorawa kwamitin Alhakin aikin tsara yadda za’a samar daga Kwalegin da inda za’a samar da ita da Kuma tabbatar da tsarin karantarwa a Kwalegin da dai sauransu.
Da yake jawabi bayan mika masa takardar shaidar kama aiki Shugaban kwamitin Farfesa Abdulsalam Nasidi ya ce an samar da kwamitin a lokacin daya dace, idan akai la’akari da yawan al’umma da kuma karancin jami’an kula da lafiya a Kano.
Ya kuma ce bada tabbacin zasu yi aiki kamar yadda ya kamata domin tabbatar da samar da Kwalegin, Inda yace zasu kammala aikin cikin wata guda kamar yadda Gwamnan ya bukata.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp