Home General Gwamnatin Jihar Kano Zata samar da Sabuwar Kwalejin koyar da harkokin Lafiya

Gwamnatin Jihar Kano Zata samar da Sabuwar Kwalejin koyar da harkokin Lafiya

Gwamnan jihar kano Dr Abdullahi Umar ya kaddamar da wani kwamiti da zai duba tare da yadda za’a samar da wata sabuwar Kwalegin koyar da harkokin kiwon lafiya domin magance matsalolin rashin Likitoci a kano da ma Nigeria baki daya.
Gwamna Ganduje ya kaddamar da kwamitin ne Mai mutane 19 yayin taron majalisar zartarwar ta jiha na wannnan makon wanda ya gudana a gidan gwamnatin jihar kano.
Ganduje ya bukaci yan kwamitin da su zage damtse wajen sauke nauyin da aka dora musu akan lokaci duba da muhimmanci da yadda al’ummar jihar kano ke bukatar Kwalegin saboda karacin jami’an lafiya da ake fama da su.
Ya ce an dorawa kwamitin Alhakin aikin tsara yadda za’a samar daga Kwalegin da inda za’a samar da ita da Kuma tabbatar da tsarin karantarwa a Kwalegin da dai sauransu.
Da yake jawabi bayan mika masa takardar shaidar kama aiki Shugaban kwamitin Farfesa Abdulsalam Nasidi ya ce an samar da kwamitin a lokacin daya dace, idan akai la’akari da yawan al’umma da kuma karancin jami’an kula da lafiya a Kano.
Ya kuma ce bada tabbacin zasu yi aiki kamar yadda ya kamata domin tabbatar da samar da Kwalegin, Inda yace zasu kammala aikin cikin wata guda kamar yadda Gwamnan ya bukata.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp